ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina Da UNICEF Za Su Yi Wa Yara Miliyan 2.8 Allurar rigakafi A Katsina 

by El-Zaharadeen Umar
7 months ago
Katsina

Asusun tallafa wa ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) da gwamnatin Jihar Katsina za su jagoranci shirya gangamin yi wa yara miliyan 2.8 allurar riga-kafin cututtuka daban-daban a Jihar Katsina.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da aka nuna buƙatar iyaye da kafafen yaɗa labarai da masu ruwa da tsaki da su ba da goyon bayan domin samun nasara.

  • Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
  • Wuta Ta Ƙone Miji, Mata Da Ƴaƴansu Ƙurmus A Katsina

Shugaban asusun UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ya buƙaci haka a lokacin wata tattaunawa da manema labarai a masaukin baƙi na Albustan Hotel da ke Katsina

ADVERTISEMENT

Kazalika, Rahama ya yaba wa gwamnatin jihar bisa irin gagarumin ci gaba wajen yaƙi da cutar shan inna da take yi, inda ya ce yanzu an samu nasarar da kusan Kashi 90 cikin ɗari.

A cewarsa, asusun UNICEF na sane da irin gudunmawar da kafofin yaɗa labarai suke bayarwa wajen wannan muhimmin aiki, wanda ya ce za su ci gaba da gangami domin tabbatar da samun ingantaciyar kiwon lafiyar al’ummar jihar Katsina.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Shugaban asusun UNICEF na ofishin Kano ya ƙara da cewa rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa tana da muhimmanci sosai musamman a kafafen sada zumunta na soshiyal midiya wajen faɗakar da al’umma kan su kai ‘ya’yansu allurar riga-kafi.

Tunda farko da yake jawabi, shugaban hukumar lafiya a matakin farko na Jihar Katsina, Dakta Shansudeen Yahaya ya sake tabbatar da ƙudirin gwamnatin Jihar Katsina na ƙare lafiyar ƙananan yara a faɗin jihar.

Dakta Shansudeen wanda ya samu wakilcin Dakta Mukhtar Mahmud ya bayyana wannan gangami da za a yi da cewa zai haɗa ƙananan hukumomi 34 na Jihar Katsina.

Ya ce akwai muhimman abubuwa da za a gudanar da suka haɗa da riga-kafin shan inna da riga-kafin cututtuka na yau da kullum da rarraba magunguna da bayar da sinadarin Ɓitamin A da taimakon lafiyar uwa da jariri.

Taro dai ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkar kiwon lafiya da suka haɗa da babban mashawarcin ƙasa kuma shugaban foliyo, Dakta Suleiman Haladu da shugabannin foliyo na sashin bayar da agajin gaggawa da sauran ƙwararru waɗanda suka jaddada buƙatar haɗin kan al’umma domin samun nasara.

Katsina
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Bam Ya Kashe Matasa 4 A Garin Banki

Bam Ya Kashe Matasa 4 A Garin Banki

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.