Asusun tallafa wa ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) da gwamnatin Jihar Katsina za su jagoranci shirya gangamin yi wa yara miliyan 2.8 allurar riga-kafin cututtuka daban-daban a Jihar Katsina.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da aka nuna buƙatar iyaye da kafafen yaɗa labarai da masu ruwa da tsaki da su ba da goyon bayan domin samun nasara.
- Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
- Wuta Ta Ƙone Miji, Mata Da Ƴaƴansu Ƙurmus A Katsina
Shugaban asusun UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ya buƙaci haka a lokacin wata tattaunawa da manema labarai a masaukin baƙi na Albustan Hotel da ke Katsina
Kazalika, Rahama ya yaba wa gwamnatin jihar bisa irin gagarumin ci gaba wajen yaƙi da cutar shan inna da take yi, inda ya ce yanzu an samu nasarar da kusan Kashi 90 cikin ɗari.
A cewarsa, asusun UNICEF na sane da irin gudunmawar da kafofin yaɗa labarai suke bayarwa wajen wannan muhimmin aiki, wanda ya ce za su ci gaba da gangami domin tabbatar da samun ingantaciyar kiwon lafiyar al’ummar jihar Katsina.
Shugaban asusun UNICEF na ofishin Kano ya ƙara da cewa rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa tana da muhimmanci sosai musamman a kafafen sada zumunta na soshiyal midiya wajen faɗakar da al’umma kan su kai ‘ya’yansu allurar riga-kafi.
Tunda farko da yake jawabi, shugaban hukumar lafiya a matakin farko na Jihar Katsina, Dakta Shansudeen Yahaya ya sake tabbatar da ƙudirin gwamnatin Jihar Katsina na ƙare lafiyar ƙananan yara a faɗin jihar.
Dakta Shansudeen wanda ya samu wakilcin Dakta Mukhtar Mahmud ya bayyana wannan gangami da za a yi da cewa zai haɗa ƙananan hukumomi 34 na Jihar Katsina.
Ya ce akwai muhimman abubuwa da za a gudanar da suka haɗa da riga-kafin shan inna da riga-kafin cututtuka na yau da kullum da rarraba magunguna da bayar da sinadarin Ɓitamin A da taimakon lafiyar uwa da jariri.
Taro dai ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkar kiwon lafiya da suka haɗa da babban mashawarcin ƙasa kuma shugaban foliyo, Dakta Suleiman Haladu da shugabannin foliyo na sashin bayar da agajin gaggawa da sauran ƙwararru waɗanda suka jaddada buƙatar haɗin kan al’umma domin samun nasara.














