ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

by Khalid Idris Doya
9 hours ago
Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sauya sunan Jami’ar Kimiyyar Lafiya mallakin Gwamnatin Tarayya da ke Azare zuwa sunan Sheikh Dahiru Usman Bauchi domin tunawa da marigayin. 

Tinubu ya misalta marigayin a matsayin babban malamin da ya hidimta wa addinin Musulunci wanda ya yi aiki domin Allah.

  • Ban Dogara Da Harkar Fim Shi Kadai A Rayuwata Ba — Maryam Usman(2)
  • An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

Shugaban ƙasar ya tabbatar da cewa Sheikh Dahiru ya yi tasiri sosai wajen inganta harkokin ilimin al’ummar Bauchi da ma Nijeriya baki ɗaya.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, ya ce, magayin ya rungumi ɗa’a ta ƙwarai wanda ya yi amfani da rayuwarsa cikin dattako da kamala.

Shugaban wanda ya ziyarci Jihar Bauchi a ranar Asabar, domin jajanta wa iyalan marigayin bisa rashin da suka yi, ya misalta rasuwar a matsayin babban rashi ga kasa baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

Ƴansanda Sun Tsaurara MatakanTsaro A Borno Gabanin Ziyarar Tinubu

Tinubu, ya ƙara da cewa Sheikh Dahiru ya kasance mutum mai ƙima wanda ya sanya kishi da son Nijeriya a zuciyarsa.

Shugaban ƙasar ya yi amfani da damar wajen kira ga al’umma da su ci gaba da yi wa ƙasar nan addu’ar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali, tare da bunƙasar tattalin arziƙi, ci gaba da rayuwa mai inganci.

Ya yi addu’ar Allah Ya jiƙan malamin, ya kuma sanya shi a Aljanna maɗaukakiya.

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad, ya nuna farin cikinsa da karamcin da shugaban ƙasar ya yi wa iyalan .amacin da kuma al’umman jihar, tun daga lokacin rasuwar malamin har zuwa yau da ya zo jihar da kansa domin jajantawa duk da tawagogin da ya yi ta turowa.

Da yake magana a madadin iyalan marigayin, Khalifansa Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ce tabbas ba za su taɓa mantawa da mutuntawa da karamcin da shugaban ƙasa ya musu ba.

Dakta Bashir Sheikh Dahiru Usman Bauchi, shi ne ya miƙa saƙon a madadin Khalifan, ya ce tun ranar jana’izar mahaifinsu Tinubu ya turo tawaga ta musamman ƙarƙashin mataimakinsa, Kashim Shettima domin halartar jana’izar daga baya kuma ya sake turo tawaga domin yi musu ta’aziyya.

“Yau kuma ga shi da kansa ka zo domin jajanta mana gaskiya mun gode da wannan karamci.”

“A madadin dukkanin iyalan Sheikh Dahiru Usman Bauchi, mabiya da magoya bayansa, tabbas muna miƙa godiya ta musamman ga shugaban ƙasa bisa karamcin da ya yi  mana.”

Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Ƴansanda Sun Tsaurara MatakanTsaro A Borno Gabanin Ziyarar Tinubu
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Tsaurara MatakanTsaro A Borno Gabanin Ziyarar Tinubu

December 20, 2025
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Borno Ranar Asabar Don Ƙaddamar Da Aiyuka

December 20, 2025
Next Post
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

December 20, 2025
Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.