ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

by Khalid Idris Doya
6 months ago
Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sauya sunan Jami’ar Kimiyyar Lafiya mallakin Gwamnatin Tarayya da ke Azare zuwa sunan Sheikh Dahiru Usman Bauchi domin tunawa da marigayin. 

Tinubu ya misalta marigayin a matsayin babban malamin da ya hidimta wa addinin Musulunci wanda ya yi aiki domin Allah.

  • Ban Dogara Da Harkar Fim Shi Kadai A Rayuwata Ba — Maryam Usman(2)
  • An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

Shugaban ƙasar ya tabbatar da cewa Sheikh Dahiru ya yi tasiri sosai wajen inganta harkokin ilimin al’ummar Bauchi da ma Nijeriya baki ɗaya.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, ya ce, magayin ya rungumi ɗa’a ta ƙwarai wanda ya yi amfani da rayuwarsa cikin dattako da kamala.

Shugaban wanda ya ziyarci Jihar Bauchi a ranar Asabar, domin jajanta wa iyalan marigayin bisa rashin da suka yi, ya misalta rasuwar a matsayin babban rashi ga kasa baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

Tinubu, ya ƙara da cewa Sheikh Dahiru ya kasance mutum mai ƙima wanda ya sanya kishi da son Nijeriya a zuciyarsa.

Shugaban ƙasar ya yi amfani da damar wajen kira ga al’umma da su ci gaba da yi wa ƙasar nan addu’ar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali, tare da bunƙasar tattalin arziƙi, ci gaba da rayuwa mai inganci.

Ya yi addu’ar Allah Ya jiƙan malamin, ya kuma sanya shi a Aljanna maɗaukakiya.

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad, ya nuna farin cikinsa da karamcin da shugaban ƙasar ya yi wa iyalan .amacin da kuma al’umman jihar, tun daga lokacin rasuwar malamin har zuwa yau da ya zo jihar da kansa domin jajantawa duk da tawagogin da ya yi ta turowa.

Da yake magana a madadin iyalan marigayin, Khalifansa Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ce tabbas ba za su taɓa mantawa da mutuntawa da karamcin da shugaban ƙasa ya musu ba.

Dakta Bashir Sheikh Dahiru Usman Bauchi, shi ne ya miƙa saƙon a madadin Khalifan, ya ce tun ranar jana’izar mahaifinsu Tinubu ya turo tawaga ta musamman ƙarƙashin mataimakinsa, Kashim Shettima domin halartar jana’izar daga baya kuma ya sake turo tawaga domin yi musu ta’aziyya.

“Yau kuma ga shi da kansa ka zo domin jajanta mana gaskiya mun gode da wannan karamci.”

“A madadin dukkanin iyalan Sheikh Dahiru Usman Bauchi, mabiya da magoya bayansa, tabbas muna miƙa godiya ta musamman ga shugaban ƙasa bisa karamcin da ya yi  mana.”

Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Tinubu
Manyan Labarai

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya
Manyan Labarai

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Next Post
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.