ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

by Khalid Idris Doya
9 months ago
Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sauya sunan Jami’ar Kimiyyar Lafiya mallakin Gwamnatin Tarayya da ke Azare zuwa sunan Sheikh Dahiru Usman Bauchi domin tunawa da marigayin. 

Tinubu ya misalta marigayin a matsayin babban malamin da ya hidimta wa addinin Musulunci wanda ya yi aiki domin Allah.

  • Ban Dogara Da Harkar Fim Shi Kadai A Rayuwata Ba — Maryam Usman(2)
  • An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

Shugaban ƙasar ya tabbatar da cewa Sheikh Dahiru ya yi tasiri sosai wajen inganta harkokin ilimin al’ummar Bauchi da ma Nijeriya baki ɗaya.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, ya ce, magayin ya rungumi ɗa’a ta ƙwarai wanda ya yi amfani da rayuwarsa cikin dattako da kamala.

Shugaban wanda ya ziyarci Jihar Bauchi a ranar Asabar, domin jajanta wa iyalan marigayin bisa rashin da suka yi, ya misalta rasuwar a matsayin babban rashi ga kasa baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Tinubu, ya ƙara da cewa Sheikh Dahiru ya kasance mutum mai ƙima wanda ya sanya kishi da son Nijeriya a zuciyarsa.

Shugaban ƙasar ya yi amfani da damar wajen kira ga al’umma da su ci gaba da yi wa ƙasar nan addu’ar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali, tare da bunƙasar tattalin arziƙi, ci gaba da rayuwa mai inganci.

Ya yi addu’ar Allah Ya jiƙan malamin, ya kuma sanya shi a Aljanna maɗaukakiya.

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad, ya nuna farin cikinsa da karamcin da shugaban ƙasar ya yi wa iyalan .amacin da kuma al’umman jihar, tun daga lokacin rasuwar malamin har zuwa yau da ya zo jihar da kansa domin jajantawa duk da tawagogin da ya yi ta turowa.

Da yake magana a madadin iyalan marigayin, Khalifansa Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ce tabbas ba za su taɓa mantawa da mutuntawa da karamcin da shugaban ƙasa ya musu ba.

Dakta Bashir Sheikh Dahiru Usman Bauchi, shi ne ya miƙa saƙon a madadin Khalifan, ya ce tun ranar jana’izar mahaifinsu Tinubu ya turo tawaga ta musamman ƙarƙashin mataimakinsa, Kashim Shettima domin halartar jana’izar daga baya kuma ya sake turo tawaga domin yi musu ta’aziyya.

“Yau kuma ga shi da kansa ka zo domin jajanta mana gaskiya mun gode da wannan karamci.”

“A madadin dukkanin iyalan Sheikh Dahiru Usman Bauchi, mabiya da magoya bayansa, tabbas muna miƙa godiya ta musamman ga shugaban ƙasa bisa karamcin da ya yi  mana.”

Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.