ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

by Sani Anwar
6 months ago
Kotu

Jami’ar Maryam Abacha da ke Kano (MAAUN), ta fuskantar matsanancin bincike daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Kano, kan harajin da ta kakaba wa daliban da ta yaye na kimanin naira 750,000.

Hukumar kula da jami’ar mai zaman kanta da ke Kano, ta tilasta wa daliban da ta yaye biyan wadannan makudan kudade, kafin bayar da sakamakon karshe da kuma tura sunayensu zuwa hukumar NYSC da kuma ba su sauran takardun da suka dace kafin yaye daliban, lamarin da ya sa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta shiga tsakani.

  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • ‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

Hukumar korafe-korafen da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, ta umarci jami’ar ta da dakatar da bukatar ta karbar Naira 750,000 daga hannun daliban.

ADVERTISEMENT

A wata wasika mai dauke da kwanan watan 27 ga watan Nuwamban 2025, mai dauke da sa hannun shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Salisu Saleh, an umarci jami’ar da ta dakatar da karbar wadannan kudade tare da bai wa daliban takardar shedar tafiya bautar kasa (NYSC) da kuma takardar shedar kammala karatun jami’ar.

Hukumar ta bayyana a cikin wasikar cewa, tana daukar matakin ne daidai da ikonta a karkashin sashe na 9 da 15 na dokar PCACC ta 2008 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima, 2010), da kuma hana ayyukan da ka iya kawo cikas ga binciken.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Hukumar ta tabbatar da samun korafi a hukumance game da sanya kudaden da kuma damuwar cewa, akwai barazanar hukunta daliban sakamakon kin biyan kudin.

Duk da umarnin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta bayar, iyayen daliban da aka yaye, sun koka da rashin mutunta sanarwar, kamar yadda hukumar gwamnati ta bayar, inda a maimakon haka jami’ar ta yi musu barazana.

Mahaifiyar dalibin da ya kammala karatun digirin da ya nemi a sakaya sunansa ya nuna damuwarsa kan yadda mahukuntan jami’ar suka rufe kofa tare da kin amsa tambayoyi daga iyayen.

Da yake mayar da martani game da karin korafe-korafen, Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Saidu Yahya, ya tabbatar da binciken da ake yi kan lamarin tare da tabbatar da aniyar ganin cewa; ba a cutar da kowa ba.

Binciken LEADERSHIP, ta tabbatar da cewa, hukumar jami’ar ta Maryam Abacha, ta samu izinin daga kotu na dakatar da binciken hukumar korafe-korafen ta Jihar Kano kan al’amarin, har sai ta kammala bincikenta tare da yanke hukunci.

Har izuwa lokacin hada wannan rahoto, ba mu samu damar jin ta bakin hukumar jami’ar ta MAAUN din ba.

Kotu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.