ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

by Sani Anwar
9 months ago
Kotu

Jami’ar Maryam Abacha da ke Kano (MAAUN), ta fuskantar matsanancin bincike daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Kano, kan harajin da ta kakaba wa daliban da ta yaye na kimanin naira 750,000.

Hukumar kula da jami’ar mai zaman kanta da ke Kano, ta tilasta wa daliban da ta yaye biyan wadannan makudan kudade, kafin bayar da sakamakon karshe da kuma tura sunayensu zuwa hukumar NYSC da kuma ba su sauran takardun da suka dace kafin yaye daliban, lamarin da ya sa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta shiga tsakani.

  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • ‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

Hukumar korafe-korafen da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, ta umarci jami’ar ta da dakatar da bukatar ta karbar Naira 750,000 daga hannun daliban.

ADVERTISEMENT

A wata wasika mai dauke da kwanan watan 27 ga watan Nuwamban 2025, mai dauke da sa hannun shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Salisu Saleh, an umarci jami’ar da ta dakatar da karbar wadannan kudade tare da bai wa daliban takardar shedar tafiya bautar kasa (NYSC) da kuma takardar shedar kammala karatun jami’ar.

Hukumar ta bayyana a cikin wasikar cewa, tana daukar matakin ne daidai da ikonta a karkashin sashe na 9 da 15 na dokar PCACC ta 2008 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima, 2010), da kuma hana ayyukan da ka iya kawo cikas ga binciken.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Hukumar ta tabbatar da samun korafi a hukumance game da sanya kudaden da kuma damuwar cewa, akwai barazanar hukunta daliban sakamakon kin biyan kudin.

Duk da umarnin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta bayar, iyayen daliban da aka yaye, sun koka da rashin mutunta sanarwar, kamar yadda hukumar gwamnati ta bayar, inda a maimakon haka jami’ar ta yi musu barazana.

Mahaifiyar dalibin da ya kammala karatun digirin da ya nemi a sakaya sunansa ya nuna damuwarsa kan yadda mahukuntan jami’ar suka rufe kofa tare da kin amsa tambayoyi daga iyayen.

Da yake mayar da martani game da karin korafe-korafen, Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Saidu Yahya, ya tabbatar da binciken da ake yi kan lamarin tare da tabbatar da aniyar ganin cewa; ba a cutar da kowa ba.

Binciken LEADERSHIP, ta tabbatar da cewa, hukumar jami’ar ta Maryam Abacha, ta samu izinin daga kotu na dakatar da binciken hukumar korafe-korafen ta Jihar Kano kan al’amarin, har sai ta kammala bincikenta tare da yanke hukunci.

Har izuwa lokacin hada wannan rahoto, ba mu samu damar jin ta bakin hukumar jami’ar ta MAAUN din ba.

Kotu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.