• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Annobar Tura Yara Mata Aikatau!

by Sister Iyami Jalo
3 years ago
Aikatau

Kadan daga cikin matsalolin dake addabar mata musamman yara, matasa, ita ce tura su aikatau wassu garuruwa ba tare da la’akarin wadanne irin matsaloli za su fuskanta a can ba. 

Iyaye kan tura yara mata wasu garuruwa da sunan neman kudi ko samo abin duniya, wanda kafin a samu yaro namiji daya da aka tura aikatau sai an samu yara mata sama da goma da aka tura, me ya sa?

  • Malam Ina So Na Hadu Da Mijina Na Farko A Aljanna, Ko Zai Yiwu?
  • GORON JUMA’A

Yana da kyau iyaye mata su fahimci cewar ‘ya mace abar tattali ce da kulawa, tana bukatar tallafi fiye da namiji ta kowacce fuska amma iyaye ba sa duba haka.

Wasu iyaye dai bukatarsu a sama musu kudi ta kowacce hanya.

Me ya sa iyaye ke tauye rayuwar ‘ya mace? Me ya sa ba za a ba ta dama ba ta yadda za ta kula da rayuwarta da na yaran da za ta haifa a gaba ba? Inda a ce za a ba wa yara dama a ji ta ra’ayinsu fiye da rabinsu ba wai suna so ba ne ake tura su wannan aikatau din.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Matsalolin Da Tura Yara Mata Aikatau Ke Haifarwa Akwai matsaloli da tura yara mata aikatau ke haifarwa masu tarin yawa amma ga kadan daga cikin su:

1: Yana hana ta neman ilmi.

2: Yana dakushe mata mafarkinta ya hana mata cikar burinta.

3: Yana bata tarbiyya.

4: Yana mayar da ita marar ‘yanci.

5: Yana mayar da ita tamkar baiwa

6: Yana haifar da rashin tausayi a zuciyarta. Ta yadda za ta sa a ranta cewar ba a sonta ya sa aka kai ta wani wuri da sunan aiki wannan dalili sai ya kangarar mata da zuciya.

7: Yana jefa yara harkar sace -sace.

8: Wasu na fadawa harkar zinace-zinace.

9: Karshe wasu su dawo gida da ciki hade da ciwon zamani.

Ina Mafita? 

Mafita a nan ita ce:

1: Iyaye mu sani cewar duk kudin da za a yi nema ta wani gari to ana iya samunsa a gida.

2: Mu tabbata in zamu tura yara aikatau a yi yarjejeniyar ba su damar neman ilmi.

3: A rinka bibiyar halin da suke ciki a kodayaushe.

4: Mu saurare su a lokacin da muka kai musu ziyara ta nan za mu fahimci matsalarsu.

5: Mu rinka tuntubar su ta wayar hannu mu ji labarinsu.

6: Idan sun zo ganin gida mu tabbatar da mun bincike su.

7: Mu sa ido sosai don ganin halayyarsu ba ta canja ba.

8: Idan da hali mu kyale su su yi aikin kusa da mu muna ganin shiga da fitar su.

Shawara

A shawarce yana da kyau iyaye mu sa ni cewar babu alheri wurin tura yara aikatau wasu garuruwa, yara mata da yawa kan fada garari da kuncin rayuwa a lokacin da suka bar gaban iyayensu da sunan neman kudi a wurare dabandabam. Mu sani daraja da mutunci hade da rayuwar yaranmu sun fi mana komai a rayuwa. Iyaye mata a kula da wannan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
Labarai

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
Manyan Labarai

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa
Manyan Labarai

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
Next Post
Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.