ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Xi

Da safiyar yau Talata 14 ga watan nan na Oktoba, shugaban kasar Xi Jinping ya gana da takwaransa na Ghana John Dramani Mahama a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, wanda ya zo kasar Sin domin halartar taron kolin mata na duniya.

 

Xi ya bayyana cewa, a bana ake cika shekaru 65 da kafa alakar diflomasiyya tsakanin Sin da Ghana. Ya kuma bukaci bangarorin biyu su tabbatar da sakamakon taron kolin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, tare da binciko hanyoyin hadin gwiwa iri-iri, da fadada hadin gwiwa a fannonin hakar ma’adinai da makamashi da gina kayayyakin more rayuwa, da aikin gona da na kamun kifi.

ADVERTISEMENT

 

Ya ce bangarorin sun cimma matsaya daya kan tsai da yarjejeniyar raya huldar abota ta ci gaban tattalin arziki a bangaren samun riba a mataki na farko, kana ya yi fatan Ghana za ta samu fa’ida daga matakin Sin na soke haraji kan kayayyakin dake shiga kasar daga kasashen Afirka masu alaka da ita.

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

 

A nasa bangaren, shugaba Mahama ya taya Sin murnar cimma nasarar gudanar da taron kolin mata na duniya. Yana mai cewa taron yana da muhimmanci, kuma ya bayyana karfin jagorancin Sin na daga matsayin ayyukan mata a duniya. Ya ce Ghana tana da dadaddiyar dangantakar abota da Sin, kana ya godewa Sin saboda goyon baya, da taimako da take baiwa mata karkashin taron FOCAC, da kuma shawarar “ziri daya da hanya daya”. Shugaba na Ghana ya yi fatan kara yin hadin gwiwa da Sin a fannonin kasuwanci, da tattalin arzikin dijital, da gina kayayyakin more rayuwa, da kuma makamashi, da hakar ma’adinai da musayar al’adu, domin inganta dangantakar kasashen biyu.

 

A wannan rana kuwa, shugaba Xi Jinpng ya gana da firaministar kasar Mozambique Maria Benvinda Delfina Levi, wadda take halartar taron koli na mata na duniya dake gudana yanzu haka a birnin Beijing.

 

Yayin zantawarsu, shugaba Xi ya ce a bana ake cika shekaru 50, da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Mozambique, kuma kawancen gargajiya tsakanin sassan biyu ya jure al’amuran kasa da kasa da dama, yana kuma ci gaba da kasancewa mai karfin gaske.

Ya ce Sin a shirye take ta yaukaka goyon bayan juna tare da Mozambique, da karfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da fadada hadin gwiwar cimma moriyar juna, da ci gaba da zurfafa cikakkiyar huldar kawance daga dukkanin fannoni, da hada hannu wajen raya sabbin shekaru 50 masu zuwa tare.

A nata bangare kuwa, Levy ta ce jawabin da shugaba Xi Jinping ya gabatar yayin taron koli na mata na duniya dake gudana, na da matukar tasiri da ma’ana. Kuma Mozambique a shirye take ta yi aiki tare da Sin wajen aiwatar da sakamakon taron, da ingiza ci gaban harkokin mata a matakin duniya.(Amina Xu、Saminu Alhassan)

Xi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Xi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.