ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Xi

Da safiyar yau Talata 14 ga watan nan na Oktoba, shugaban kasar Xi Jinping ya gana da takwaransa na Ghana John Dramani Mahama a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, wanda ya zo kasar Sin domin halartar taron kolin mata na duniya.

 

Xi ya bayyana cewa, a bana ake cika shekaru 65 da kafa alakar diflomasiyya tsakanin Sin da Ghana. Ya kuma bukaci bangarorin biyu su tabbatar da sakamakon taron kolin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, tare da binciko hanyoyin hadin gwiwa iri-iri, da fadada hadin gwiwa a fannonin hakar ma’adinai da makamashi da gina kayayyakin more rayuwa, da aikin gona da na kamun kifi.

ADVERTISEMENT

 

Ya ce bangarorin sun cimma matsaya daya kan tsai da yarjejeniyar raya huldar abota ta ci gaban tattalin arziki a bangaren samun riba a mataki na farko, kana ya yi fatan Ghana za ta samu fa’ida daga matakin Sin na soke haraji kan kayayyakin dake shiga kasar daga kasashen Afirka masu alaka da ita.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

 

A nasa bangaren, shugaba Mahama ya taya Sin murnar cimma nasarar gudanar da taron kolin mata na duniya. Yana mai cewa taron yana da muhimmanci, kuma ya bayyana karfin jagorancin Sin na daga matsayin ayyukan mata a duniya. Ya ce Ghana tana da dadaddiyar dangantakar abota da Sin, kana ya godewa Sin saboda goyon baya, da taimako da take baiwa mata karkashin taron FOCAC, da kuma shawarar “ziri daya da hanya daya”. Shugaba na Ghana ya yi fatan kara yin hadin gwiwa da Sin a fannonin kasuwanci, da tattalin arzikin dijital, da gina kayayyakin more rayuwa, da kuma makamashi, da hakar ma’adinai da musayar al’adu, domin inganta dangantakar kasashen biyu.

 

A wannan rana kuwa, shugaba Xi Jinpng ya gana da firaministar kasar Mozambique Maria Benvinda Delfina Levi, wadda take halartar taron koli na mata na duniya dake gudana yanzu haka a birnin Beijing.

 

Yayin zantawarsu, shugaba Xi ya ce a bana ake cika shekaru 50, da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Mozambique, kuma kawancen gargajiya tsakanin sassan biyu ya jure al’amuran kasa da kasa da dama, yana kuma ci gaba da kasancewa mai karfin gaske.

Ya ce Sin a shirye take ta yaukaka goyon bayan juna tare da Mozambique, da karfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da fadada hadin gwiwar cimma moriyar juna, da ci gaba da zurfafa cikakkiyar huldar kawance daga dukkanin fannoni, da hada hannu wajen raya sabbin shekaru 50 masu zuwa tare.

A nata bangare kuwa, Levy ta ce jawabin da shugaba Xi Jinping ya gabatar yayin taron koli na mata na duniya dake gudana, na da matukar tasiri da ma’ana. Kuma Mozambique a shirye take ta yi aiki tare da Sin wajen aiwatar da sakamakon taron, da ingiza ci gaban harkokin mata a matakin duniya.(Amina Xu、Saminu Alhassan)

Xi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Xi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.