ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ki Bayar Da Belin Wanda Ya Yi Sanadin Rasa Kafar Fatima

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Kotu

Babban lauuyan gwamnatin Jihar Sakkwato kuma Kwamishinan Shari’a, Barista Sulaiman Usman (SAN), ya karbi ragamar gudanar da shari’ar da aka shigar a na karar Aliyu Sanusi Umar wanda ya kade daliba Fatima Sulaiman ‘yar shekaru 16 wanda hakan ya zama silar yanke mata kafa. 

An gurfanar da Umar ne a gaban Babbar Kotun Majistare da ke Arkilla a bisa ga tukin ganganci, tuki ba tare da lasisi ba tare da yi wa Fatima babbar illa a gaban makarantusu bayan ta kammala rubuta jarabawar karshe.

  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Kauyuka 21 A Sakkwato
  • An Gano Ayyukan Kutsen Yanar Gizo Da NSA Ta Amurka Ta Yi Wa Wata Jami’ar Kasar Sin

A zaman kotun a jiya, Babban Lauyan Gwamnati, a baki ya bukaci kotun da ta ba shi damar karbar shari’ar bisa ga dogaro da sashe na 211 na tsarin mulkin Kasa na 1999 da kuma sashe na 106 na Kundin dokar shari’a ta Jihar Sakkwato.

ADVERTISEMENT

Babban Lauyan Gwamnatin wanda ya samu wakilcin Barista Sufyanu Umar Mai- Kulki ya bayyana cewar kundin dokokin da ya gabatar, sun bashi damar karbar ragamar duk wata shari’ar miyagun laifuka wadda wani ko wata Hukuma ta shigar.

Haka ma Lauyan ya bukaci kotun da ta dage sauraren shari’ar zuwa mako daya domin ba shi damar shiryawa shari’ar yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Sai dai Lauyan mai kariya, Jacob Ochidi (SAN) ya nuna rashin aminta da bukatar karbar shari’ar a baki yana cewar tun farko kotu ta aminta da gudanar da sauri a shari’ar daga ranar Talata. Ya ce idan har ba za a gaggauta shari’ar ba, to a bayar da belin wanda yake kariya domin a cewarsa ga alamu za a tsawaita shari’ar.

Da take yanke hukunci kan matsayar kotu, Mariya Haruna Dogon-Daji ta sa kafa ta yi fatali da bukatar bayar da wanda ke kariya beli ta na cewar an yi sauri idan aka bayar da belinsa a wannan lokacin. A kan wannan ta dage zaman kotun zuwa ranar 19 ga Satumba tare da bayar da umurnin ci-gaba da tsare wanda ake tuhuma a gidan gyara hali.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Next Post
Dubban Mutane Sun Yi Zanga-Zangar Adawa Da Mulkin Soji A Sudan

Dubban Mutane Sun Yi Zanga-Zangar Adawa Da Mulkin Soji A Sudan

LABARAI MASU NASABA

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.