• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoton EU Game Da Hong Kong Na Cike Da Yaudara

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Rahoton EU Game Da Hong Kong Na Cike Da Yaudara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Har kullum kasashen yammacin duniya na nacewa manufofin nuna yatsa ga kasar Sin, ta hanyar fakewa da yayata dimokaradiyya, ko kare hakkin bil adama, duk kuwa da irin nasu tarin matsalolin na cikin gida.

A baya bayan nan, wani rahoto da Tarayyar Turai EU ta fitar mai taken “Rahoton shekara game da yankin musamman na Hong Kong na shekarar 2021”, ya kunshi bayanai masu tarin yawa, da EUn ke ikirarin haka ya kamata kasar Sin ta rika tafiyar da harkoki a yankin na HK.

Wannan rahoto, wanda shi ne irinsa na 24 da EUn ta fitar, na kunshe da kalamai na yaudara da suka saba da gaskiya, ciki har da zargin wai “yanayin kare hakkin bil adama na kara tabarbarewa a yankin na HK”.

Amma abun tambaya a nan shi ne, ko Tarayyar Turai EU, ta taba fitar da makamancin wannan rahoto game da HK cikin shekaru sama da 140 da Birtaniya ta mulkin yankin, karkashin mulkin danniya da watsi da dimokaradiyya?
Idan da a ce kasar Sin ce ta fitar da makamancin wannan rahoto, game da bukatar gyara yanayin gudanar da mulki a Turai, da magance matsalolin dake yawan haifar da zanga-zanga, da fito-na-fito da mahukunta a Turai, da gazawar gwamnatocin Turai wajen shawo kan annoba yadda ya kamata, manya kasashe mambobin EU za su yi maraba da wannan rahoto?

Kowa ya sani cewa, a lokuta mabambanta, wasu daga kasashe mambobin kungiyar EU, sun fuskanci matsalolin tsaro makamantan wadanda Sin ta fuskanta a yankin musamman na HK. Ga misali, kasar Faransa ta sha fama da zanga zanga da fito-na-fito sakamakon dalilai na siyasa, tun daga watan Nuwamban shekarar 2018. Ya zuwa tsakiyar shekarar 2019, tashe-tashen hankula sun haifar da rasuwar mutane 11, da jikkatar fararen hula 2,500, baya ga jami’an tsaro 1,800 da su ma suka jikkata. Kaza lika an cafke adadin mutane da yawansu ya kai sama da 8,000.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Rahotanni sun ce an yi amfani da karfin tuwo wajen tabbatar da doka da oda. Inda mahukuntan Faransa suka rika barazanar daukar matakan ba-sani-ba-sabo kan masu tayar da kayar baya.
Sai dai abun mamaki a nan shi ne, da yawa daga kafofin watsa labaran kasar Faransa, sun rika kiran barnata gine-gine da masu zanga zangar suka yi a birnin Paris a wancan lokaci, da aikin tsageru, amma a daya hannun, sun rika kiran matakin lalata zauren majalisar dokokin yankin HK da masu zanga-zanga suka yi da “jarunta” shin wannan ba nuna fuska biyu ba ne?

Amfani da irin wannan mizani 2 wajen kwatanta abubuwa makamantan juna, da wariya, da kaucewa adalci daga gwamnatoci da kafafen watsa labaran kasashen yamma suke yi, ya yi daidai da karin maganar Bahaushe dake cewa “Laifi tudu ne, ka take naka ka hango na wani”.

Har kullum, sassa daban daban na kasashen yammacin duniya na yawan maimaita muhimmancin kare hakkin bil adama. Amma sun mance cewa, lullube laifukan da suke aikatawa na keta hakkin bil adama, da kokarin ganin baiken kasar Sin kan hakkin bil adama, yana kara fallasa aniyar su ta siyasantar da batun hakkin bil adama. Kuma irin wadannan rahotanni masu cike da kage, da rashin adalci da EU ke fitarwa, ba za su sauya hakikanin gaskiyar da dukkanin al’ummun duniya suka sani ba. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Alkaluma Sun Bayyana A Zahiri

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Korar Jirgin Sojan Australiya

Related

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya
Daga Birnin Sin

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

8 hours ago
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu
Daga Birnin Sin

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

9 hours ago
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

9 hours ago
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

11 hours ago
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575
Daga Birnin Sin

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

13 hours ago
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

13 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Korar Jirgin Sojan Australiya

Ma'aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Korar Jirgin Sojan Australiya

LABARAI MASU NASABA

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

June 18, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

June 17, 2025
An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

June 17, 2025
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

June 17, 2025
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

June 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.