ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoton EU Game Da Hong Kong Na Cike Da Yaudara

by CMG Hausa
4 years ago
Eu

Har kullum kasashen yammacin duniya na nacewa manufofin nuna yatsa ga kasar Sin, ta hanyar fakewa da yayata dimokaradiyya, ko kare hakkin bil adama, duk kuwa da irin nasu tarin matsalolin na cikin gida.

A baya bayan nan, wani rahoto da Tarayyar Turai EU ta fitar mai taken “Rahoton shekara game da yankin musamman na Hong Kong na shekarar 2021”, ya kunshi bayanai masu tarin yawa, da EUn ke ikirarin haka ya kamata kasar Sin ta rika tafiyar da harkoki a yankin na HK.

Wannan rahoto, wanda shi ne irinsa na 24 da EUn ta fitar, na kunshe da kalamai na yaudara da suka saba da gaskiya, ciki har da zargin wai “yanayin kare hakkin bil adama na kara tabarbarewa a yankin na HK”.

ADVERTISEMENT

Amma abun tambaya a nan shi ne, ko Tarayyar Turai EU, ta taba fitar da makamancin wannan rahoto game da HK cikin shekaru sama da 140 da Birtaniya ta mulkin yankin, karkashin mulkin danniya da watsi da dimokaradiyya?
Idan da a ce kasar Sin ce ta fitar da makamancin wannan rahoto, game da bukatar gyara yanayin gudanar da mulki a Turai, da magance matsalolin dake yawan haifar da zanga-zanga, da fito-na-fito da mahukunta a Turai, da gazawar gwamnatocin Turai wajen shawo kan annoba yadda ya kamata, manya kasashe mambobin EU za su yi maraba da wannan rahoto?

Kowa ya sani cewa, a lokuta mabambanta, wasu daga kasashe mambobin kungiyar EU, sun fuskanci matsalolin tsaro makamantan wadanda Sin ta fuskanta a yankin musamman na HK. Ga misali, kasar Faransa ta sha fama da zanga zanga da fito-na-fito sakamakon dalilai na siyasa, tun daga watan Nuwamban shekarar 2018. Ya zuwa tsakiyar shekarar 2019, tashe-tashen hankula sun haifar da rasuwar mutane 11, da jikkatar fararen hula 2,500, baya ga jami’an tsaro 1,800 da su ma suka jikkata. Kaza lika an cafke adadin mutane da yawansu ya kai sama da 8,000.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Rahotanni sun ce an yi amfani da karfin tuwo wajen tabbatar da doka da oda. Inda mahukuntan Faransa suka rika barazanar daukar matakan ba-sani-ba-sabo kan masu tayar da kayar baya.
Sai dai abun mamaki a nan shi ne, da yawa daga kafofin watsa labaran kasar Faransa, sun rika kiran barnata gine-gine da masu zanga zangar suka yi a birnin Paris a wancan lokaci, da aikin tsageru, amma a daya hannun, sun rika kiran matakin lalata zauren majalisar dokokin yankin HK da masu zanga-zanga suka yi da “jarunta” shin wannan ba nuna fuska biyu ba ne?

Amfani da irin wannan mizani 2 wajen kwatanta abubuwa makamantan juna, da wariya, da kaucewa adalci daga gwamnatoci da kafafen watsa labaran kasashen yamma suke yi, ya yi daidai da karin maganar Bahaushe dake cewa “Laifi tudu ne, ka take naka ka hango na wani”.

Har kullum, sassa daban daban na kasashen yammacin duniya na yawan maimaita muhimmancin kare hakkin bil adama. Amma sun mance cewa, lullube laifukan da suke aikatawa na keta hakkin bil adama, da kokarin ganin baiken kasar Sin kan hakkin bil adama, yana kara fallasa aniyar su ta siyasantar da batun hakkin bil adama. Kuma irin wadannan rahotanni masu cike da kage, da rashin adalci da EU ke fitarwa, ba za su sauya hakikanin gaskiyar da dukkanin al’ummun duniya suka sani ba. (Fa’iza Mustapha)

Eu
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Korar Jirgin Sojan Australiya

Ma'aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Korar Jirgin Sojan Australiya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.