ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoton EU Game Da Hong Kong Na Cike Da Yaudara

by CMG Hausa
4 years ago
Eu

Har kullum kasashen yammacin duniya na nacewa manufofin nuna yatsa ga kasar Sin, ta hanyar fakewa da yayata dimokaradiyya, ko kare hakkin bil adama, duk kuwa da irin nasu tarin matsalolin na cikin gida.

A baya bayan nan, wani rahoto da Tarayyar Turai EU ta fitar mai taken “Rahoton shekara game da yankin musamman na Hong Kong na shekarar 2021”, ya kunshi bayanai masu tarin yawa, da EUn ke ikirarin haka ya kamata kasar Sin ta rika tafiyar da harkoki a yankin na HK.

Wannan rahoto, wanda shi ne irinsa na 24 da EUn ta fitar, na kunshe da kalamai na yaudara da suka saba da gaskiya, ciki har da zargin wai “yanayin kare hakkin bil adama na kara tabarbarewa a yankin na HK”.

ADVERTISEMENT

Amma abun tambaya a nan shi ne, ko Tarayyar Turai EU, ta taba fitar da makamancin wannan rahoto game da HK cikin shekaru sama da 140 da Birtaniya ta mulkin yankin, karkashin mulkin danniya da watsi da dimokaradiyya?
Idan da a ce kasar Sin ce ta fitar da makamancin wannan rahoto, game da bukatar gyara yanayin gudanar da mulki a Turai, da magance matsalolin dake yawan haifar da zanga-zanga, da fito-na-fito da mahukunta a Turai, da gazawar gwamnatocin Turai wajen shawo kan annoba yadda ya kamata, manya kasashe mambobin EU za su yi maraba da wannan rahoto?

Kowa ya sani cewa, a lokuta mabambanta, wasu daga kasashe mambobin kungiyar EU, sun fuskanci matsalolin tsaro makamantan wadanda Sin ta fuskanta a yankin musamman na HK. Ga misali, kasar Faransa ta sha fama da zanga zanga da fito-na-fito sakamakon dalilai na siyasa, tun daga watan Nuwamban shekarar 2018. Ya zuwa tsakiyar shekarar 2019, tashe-tashen hankula sun haifar da rasuwar mutane 11, da jikkatar fararen hula 2,500, baya ga jami’an tsaro 1,800 da su ma suka jikkata. Kaza lika an cafke adadin mutane da yawansu ya kai sama da 8,000.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Rahotanni sun ce an yi amfani da karfin tuwo wajen tabbatar da doka da oda. Inda mahukuntan Faransa suka rika barazanar daukar matakan ba-sani-ba-sabo kan masu tayar da kayar baya.
Sai dai abun mamaki a nan shi ne, da yawa daga kafofin watsa labaran kasar Faransa, sun rika kiran barnata gine-gine da masu zanga zangar suka yi a birnin Paris a wancan lokaci, da aikin tsageru, amma a daya hannun, sun rika kiran matakin lalata zauren majalisar dokokin yankin HK da masu zanga-zanga suka yi da “jarunta” shin wannan ba nuna fuska biyu ba ne?

Amfani da irin wannan mizani 2 wajen kwatanta abubuwa makamantan juna, da wariya, da kaucewa adalci daga gwamnatoci da kafafen watsa labaran kasashen yamma suke yi, ya yi daidai da karin maganar Bahaushe dake cewa “Laifi tudu ne, ka take naka ka hango na wani”.

Har kullum, sassa daban daban na kasashen yammacin duniya na yawan maimaita muhimmancin kare hakkin bil adama. Amma sun mance cewa, lullube laifukan da suke aikatawa na keta hakkin bil adama, da kokarin ganin baiken kasar Sin kan hakkin bil adama, yana kara fallasa aniyar su ta siyasantar da batun hakkin bil adama. Kuma irin wadannan rahotanni masu cike da kage, da rashin adalci da EU ke fitarwa, ba za su sauya hakikanin gaskiyar da dukkanin al’ummun duniya suka sani ba. (Fa’iza Mustapha)

Eu
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Korar Jirgin Sojan Australiya

Ma'aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Korar Jirgin Sojan Australiya

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.