• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Kotun Tarayya da ke zamanza a Birnin Kebbi a karkashin Jagorancin mai shari’a Baba Gana Ashigar ya tabbatar da Alhaji Haruna Saidu Dandiyo a matsayin halatacin dan takarar kujerar Sanatan Kebbi ta tsakiya a karkashin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi.

Alhaji Haruna Saidu, wanda ya shigar da karar ya kai karar Sanata Muhammad Adamu Aliero, PDP da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) domin ya gudanar da sabon zaben fidda gwani na mazabar Kebbi ta tsakiya, alhali bai mutu kuma ba bisa ya janye daga takarar ba.

  • Zabarmawa Sun Yi Gagarumin Taro A Kebbi

Ya kuma kai karar su kan sauya sunansa da sunan Sanata Muhammadu Adamu Aliero, wanda ya ce yana APC a lokacin da aka gudanar da zaben fidda gwani na farko, sabanin dokokin zaben 2022 da kundin tsarin mulkin Jam’iyyar PDP.

Yayin da yake yanke hukunci a kan karar, Mai Shari’a Baba Gana Ashigar ya yanke hukuncin

Mai shari’a Asghigar, yayin da yake gabatar da hukuncin nasa kan batutuwan da suka shafi gaba daya, ya lura cewa, ko shakka babu, a lokacin da aka gudanar da zaben fidda gwani na farko na mazabar Kebbi ta tsakiya a jam’iyyar PDP, wanda ake kara na 1 yana cikin jam’iyyar mai mulki watau APC.

Labarai Masu Nasaba

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

Ya kuma kara da cewa, bisa ga hujojin da aka gabatar a gaban kotun, wanda ya shigar da karar ya halarci zaben fidda gwani na mazabar Kebbi ta tsakiya a zaben fidda gwani na farko, inda aka zabe shi, dan takarar Sanata na jam’iyyar PDP ya samu nasarar lashe zaben da kuri’u mafi girma yayin da wanda ake kara na 1 yana a jam’iyyar APC mai mulki a yanzu. Saboda haka, kotu ta gamsu da duk hujoji da kuma rokon da mai kara,” in ji shi.

 

A nasa martani, Lauyan mai kara, Sule O.Usman (SAN), wanda ya yaba wa Alkalin da ya gabatar da wannan hukuncin wanda ya baiwa wanda yake tsayawa damar samun nasara a Shari’ar.

A cewarsa, “Mun yi murna saboda mun tunkari Kotun da ta share Mana hawaye a fuskarmu, inda kotu ta tabbatar da Saidu Haruna Dandiyo a matsayin dan takarar kujerar Sanatan Kebbi ta tsakiya a PDP.

Lauyan wanda ake kara na daya, Barista Aminu Hassan wanda ya tsayawa I K. Sanusi SAN, wanda shi ma ya yabawa mai shari’a Baba Gana Ashigar bisa hukuncin da aka yanke kuma ya yaba da aikin da ya yi masa amma ya shaida wa manema labarai cewa, Sanata Muhammad Adamu Aliero zai daukaka kara kan hukuncin.

A nasa martani, Lauyan Hukumar INEC, Barista Ahmad Bello Mahamud ya ce sun koyi darasi da yawa a cikin hukuncin kuma ya yaba wa Mai Shari’a Ashigar bisa yanke hukunci da yayi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fahimtar Juna, Ita Ce Tushen Ingantacciyar Dangantaka

Next Post

Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

Related

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

2 minutes ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

2 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

4 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

6 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

9 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

LABARAI MASU NASABA

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.