• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Kotun Tarayya da ke zamanza a Birnin Kebbi a karkashin Jagorancin mai shari’a Baba Gana Ashigar ya tabbatar da Alhaji Haruna Saidu Dandiyo a matsayin halatacin dan takarar kujerar Sanatan Kebbi ta tsakiya a karkashin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi.

Alhaji Haruna Saidu, wanda ya shigar da karar ya kai karar Sanata Muhammad Adamu Aliero, PDP da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) domin ya gudanar da sabon zaben fidda gwani na mazabar Kebbi ta tsakiya, alhali bai mutu kuma ba bisa ya janye daga takarar ba.

  • Zabarmawa Sun Yi Gagarumin Taro A Kebbi

Ya kuma kai karar su kan sauya sunansa da sunan Sanata Muhammadu Adamu Aliero, wanda ya ce yana APC a lokacin da aka gudanar da zaben fidda gwani na farko, sabanin dokokin zaben 2022 da kundin tsarin mulkin Jam’iyyar PDP.

Yayin da yake yanke hukunci a kan karar, Mai Shari’a Baba Gana Ashigar ya yanke hukuncin

Mai shari’a Asghigar, yayin da yake gabatar da hukuncin nasa kan batutuwan da suka shafi gaba daya, ya lura cewa, ko shakka babu, a lokacin da aka gudanar da zaben fidda gwani na farko na mazabar Kebbi ta tsakiya a jam’iyyar PDP, wanda ake kara na 1 yana cikin jam’iyyar mai mulki watau APC.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ya kuma kara da cewa, bisa ga hujojin da aka gabatar a gaban kotun, wanda ya shigar da karar ya halarci zaben fidda gwani na mazabar Kebbi ta tsakiya a zaben fidda gwani na farko, inda aka zabe shi, dan takarar Sanata na jam’iyyar PDP ya samu nasarar lashe zaben da kuri’u mafi girma yayin da wanda ake kara na 1 yana a jam’iyyar APC mai mulki a yanzu. Saboda haka, kotu ta gamsu da duk hujoji da kuma rokon da mai kara,” in ji shi.

 

A nasa martani, Lauyan mai kara, Sule O.Usman (SAN), wanda ya yaba wa Alkalin da ya gabatar da wannan hukuncin wanda ya baiwa wanda yake tsayawa damar samun nasara a Shari’ar.

A cewarsa, “Mun yi murna saboda mun tunkari Kotun da ta share Mana hawaye a fuskarmu, inda kotu ta tabbatar da Saidu Haruna Dandiyo a matsayin dan takarar kujerar Sanatan Kebbi ta tsakiya a PDP.

Lauyan wanda ake kara na daya, Barista Aminu Hassan wanda ya tsayawa I K. Sanusi SAN, wanda shi ma ya yabawa mai shari’a Baba Gana Ashigar bisa hukuncin da aka yanke kuma ya yaba da aikin da ya yi masa amma ya shaida wa manema labarai cewa, Sanata Muhammad Adamu Aliero zai daukaka kara kan hukuncin.

A nasa martani, Lauyan Hukumar INEC, Barista Ahmad Bello Mahamud ya ce sun koyi darasi da yawa a cikin hukuncin kuma ya yaba wa Mai Shari’a Ashigar bisa yanke hukunci da yayi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fahimtar Juna, Ita Ce Tushen Ingantacciyar Dangantaka

Next Post

Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

Related

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

4 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

6 hours ago
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami
Labarai

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

6 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

7 hours ago
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

8 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

LABARAI MASU NASABA

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.