• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

Chris Ngige

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta yi wa sababbin kungiyoyin jami’o’in Nijeriya guda biyu rajista a hukumance a matsayin kungiyoyin kasuwanci.

Wadanda suke kusa da lamarin sun bayyana cewa sababbin kungiyoyin sun kasance kishiyoyi ga kungiyar malaman jami’a’o’i ta kasa (ASUU), wadda da dage tana jayayya da gwamnatin tarayya.

  • Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
  • Gwamnatin Habasha Da ‘Yan Tawayen Tigray Za Su Zauna A Teburin Sulhu

Sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista dai sun hada da ‘Congressof Nigerian Unibersity Academics (CONUA), da ‘Nigeria Associationof Medical and Dental Lecturers in Academics (NAMDA).’

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan gabatar da takardar yi wa kungiyoyin guda biyu rajista a Abuja, Ministan kwadugo da samar da ayyukan yi, Chris Ngige, ya bayyana cewa wannan mataki yana kan tsarin dokar kasa domin shawo kan matsalolin da jami’o’in suke fuskanta.

Ngige ya kara da cewa wadannan kungiyoyi guda biyu wani bangare nena ASUU da suka balle daga jami’o’in Nijeriya, kamar yadda dokar kasa da kasa na kafa kungiyoyin mai lamba 87 da 98 ta tanada, wanda ya bai wa kungiyoyin ‘yancin kare hakkinsu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Ngige ya ce, “Ma’aikatar kwadugo da samar da ayyukan yi ta yi gaban kanta wajen fito da sababbin kungiyoyin kasuwanci domin habaka tsarin kasuwanci a cikin kasar nan tare da yanke shawarar amincewa da yi wa sabbin kungiyoyi guda biyu rajista a karkashin jami’o’in Nijeriya.

“Watanni 8 da suka gabata, jami’o’in gwamnatin tarayya suna rufe, sannan dalibai suna zaune a gida sakamakon yajin aiki da kungiyar ASUU suke yi, duk da kokarin sasantawa da gwamnatin tarayya ta yi, amma lamarin ya ci tura.

“Karkashin dokar kasuwanci na gwamnatin tarayya ta shekarar 2004,wannan yajin aiki ya kamata ya kawo karshe tun a zaman sulhu da wannan ma’aikata da yi kokarin yi a ranakun 22 ga watan Fabrairun 2022 da ranar 1 ga watan Maris ta 2022.

“Duk wani kokarin sulhu ya ci tura, sakamakon dagewa da kungiyar ASUU ta yi wanda har kotun da’ar ma’aikata ta zantar da hukunci a matsayinta da take sasanta rikici a tsakanin kungiyoyi, amma ASUU ta ki bin wannan umarni.

“Abun ban sha’awar dai shi ne, mafi yawancin malaman jami’o’in da ke karantarwa a makarantun gwamnati sun nuna sha’awarsu na komawa bakin aiki idan aka sulhunta,” Ngige.

A nasa martanin, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa sababbin kungiyoyin da aka yi wa rajista ba mambobinsu ba ne, ya dai zargi gwamnatin tarayya da yin farfaganda wajen kare laifinta a wurin ‘yan Nijeriya.

Ya kara da cewa gwamnatin tarayya tana yin dukkkan wadannan abubuwa ne saboda mambobin ASUU sun ki rakonta kan tsayar musu da albashinsu.

Hakazalika, shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari shi ne mai wuka da nama na yanke hukunci na karshe kan yajin aikin ASUU bayan ganawarsa da zauran majalisar wakilai a wannan mako.

Ya dai bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala zaman ganawar sulhu tsakanin shugaban kasa da ‘yan majalisar a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Shugaban majalisar wakilan yana fatan za a samu sulhu bayan gabatar da rahoto, inda ya roki shugabankasa ya yi nazari a rahoton kafin su sake zama da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUBuhariChris NgigeDalibaiGwamnatin TarayyaKungiyoyiMa'aikataYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Umurci Kungiyar ASUU Da Ta Gaggauta Janye Yajin Aikin Da Take

Next Post

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

56 minutes ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

7 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

10 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

11 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

19 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

1 day ago
Next Post
Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.