• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Al'ajabi
0
An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekara 2015, Sulemana Abdul Samed ya farka daga barci, amma sai wani abu ya bashi mamaki domin ya lura cewa harshensa ya kara girma har ya cika masa baki ta yadda baya iya yin numfashi sosai.

Bayan ya sha magani da ya sayo a wani kemis, wanda ya rage kumburin harshen, dan makarantar babbar sakandaren bai san cewa wannan lamarin zai sauya rayuwarsa gaba daya ba.

  • Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA
  • An Nemi Fulani Su Manta Da Bambancin Da Ke Tsakaninsu Don Kubuta Daga Matsalar Tsaro

Kuma daga wancan lokacin zuwa yanzu, Sulemana wanda aka fi sani da sunan Awuche- ya rika kara tsawo har sai da ya kai kafa 9.6 kuma ya ci gaba da kara tsawo.

“Cikin kowane wata uku zuwa wata hudu na ke kara tsawo. Idan ba ka gan ni cikin wata uku ko hudu ba, za ka na kara tsawo,” in ji Awuche yayin da yake hira da wakilin BBC Pidgin Fabour Nunoo.

Tsawon da Awuche ya yi ya sa ya zama wani shahararre a garinsu Gambaga yayin da mazauna garin daga kananansu har zuwa dattawan garin ke kallonsa da ta’ajibi.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

“Akwai lokacin da wani dan sanda ya ce nazarce shi da tsawona, saboda haka ya ce zai dauki hoto tare da ni,” kamar yadda ya tuna.

Daga ‘yan siyasa zuwa ga jami’an soji da na ‘yansanda duka suna farin ciki da zarar sunga Awuche, wanda baya ga cewa ya fi kowa tsawo, yana kuma da kyawun mu’amala da sauran jama’a.

“Tsawona ya mayar da ni sahahrarre,”kamar yadda ya shaida wa wakilin BBC wanda ya ziyarci garin na Awuche.

Ya kuma ce da a duk lokacin da ya halarci wani biki, sai mutane a wurin su rika matsowa kusa da shi kuma yana son haka sosai.

Ya kan kuma ba su damar daukar hoto da shi a duk lokacin da suka bukaci haka.

“Likitoci sun ce tsawona na lalura ce mai suna ‘gigantism’ Tsawon da Awuche ya yi ba irin wanda aka saba gani ba ne, domin ko likitoci na kiransa da sunan ‘gigantism’ da turancin Ingilishi.

Sun ce wannan matsala ce da kan sa mutum ya yi tsawon da ya zarce na yawancin mutane.

“Yayin da na je asibitin BMC, sai wani mutum farar fata ya ganni kuma sai ya ce ina da lalurar gigantism.

“Ya kuma ce wani likitan da ya rika duba lafiyarsa ya shaida masa cewa akwai wani abu a cikin kwakwalwarsa da ya kamata a yi masa tiyata domin a cire shi.

Ya ce wannan abin ne ke sa kashinsa ke kara girma da tsawo sosai, kuma ya ce idan ba a cire wannan abin daga kwakwalwarsa ba, ba zai daina tsawo ba kuma wannan kai ya shafar lafiyarsa da ingancin walwala da jin dadin rayuwarsa.

Amma duk da haka Awuche yana fatan yin aure da haihuwar ‘ya’ya, wadanda ya ce yake son ganin yadda za su kasance.

Kuma bai damu da cewa ya fi kowa tsawo ba, domin ya ce haka Allah ya so ya gan shi kenan.

Mun ciro muku daga BBC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BBCCutaDalibiMamakiMutaneTsawo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA

Next Post

Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

Related

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

2 weeks ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

1 month ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

2 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

4 months ago
Next Post
Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.