ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA

by Muhammad Awwal Umar
4 years ago
Majalisa

Sakamakon dambawar zaben kananan hukumomin Neja da majalisar dokokin jiha ta shelanta dakatar da shugaban hukumar zabe ta jiha, Alhaji Baba Aminu.

Shugaban kungiyar lauyoyin jihar, Mohammed Waziri Abdulkadir ya bayyana cewar majalisar ta yi hawan kawara ga dokar zabe ta jiha sashi na 201 da 197 na shekarar 1999 da aka yiwa gyaran fuska, dan haka ya nemi majalisar ta canja tunanin ta.

  • Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba
  • Yadda Ake Tabbatar Da Ci Gaba Mai Inganci A Birnin Shanghai Na Kasar Sin

Majalisar ta bayyana dakatar da shugaban hukumar zabe ta jiha inda suka zarge shi da rashin cancantar shugabantar hukumar NISIEC.

ADVERTISEMENT

Alh. Baba Aminu ya halarci majalisar a wani gayyatar da tai mai saboda maganar ci gaba da shirye-shiryen zaben kananan hukumomi da hukumar ke aiwatarwa a halin yanzu inda majalisar ta nemi a dakatar da zaben wanda za a gudanar a watan Nuwambar wannan shekarar.

Hukumar NISIEC na shirya zaben ne sakamakon wa’adin shugabannin kananan hukumomi zai kare watanni uku masu zuwa, kuma majalisar ta nemi a dakatar da shirya zaben sakamakon karar rashin amincewar zaben da jam’iyyar PDP ta shirgar a babban kotun tarayya da ke minna nakin amincewa da zaben a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Sakamakon tambayoyin manema labarai ga shugaban kungiyar lauyoyin jiha, Mohammed Waziri Abdulkakir ya bayyana cewar majalisar bata da hurumin dakatar da shugaban hukumar zaben, domin dakatarwar ya sabawa doka kuma bai kan ka’idar doka.

“Ba su da hurumin dakatar shugaban hukumar zabe, gwamna ne kawai ke da hurumin neman tsige shugaban ko dakatarwar, sannana samu kashi biyu bisa uku na ‘yan majalisar su amince da hakan”.

Yanzu labaran da muke samu awani zaman majalisar wanda gefe daya ne suka zartas da hukuncin.

Kora ko dakatarwar na majalisar ya fito ne daga gwamna ko majalisar dokokin ne tai gaban kan ta na dakatarwar.

Lauyan ya shawarci majalisar da su bi dokar da ta samar da hukumar da kuma bai wa hukumar shugabanci da sakataren hukumar da sauran manyan masu mukamai a hukumar, ya jawo hankalin majalisar akan dokar 1999 da ta samar da hukumar.

“Bari in sake tambaya, shin dakatarwar daga majalisar ne, domin ba wanda ke da hurumin dakatarwa ko korar shugaban hukumar zabe da sakataren hukumar sai gwamna.

Sashi na 201 ya bayyana cewar sai kashi biyu bisa uku na majalisar ta amince da kudurin, yanzu abin da wannan ke magana gwamna ne yake da hurumin neman majalisar dokokin da ta cire shugaban hukumar”.

Saboda haka abinda dokar ya ce, maganar korar shugaban hukumar zabe gwamna kawai ke da wannan damar, ina kira ga majalisar dokokin da su canja tunanin su akan korar shugaban hukumar zabe.

Abdulkadir ya bayyana cewar a zaman kungiyar na gaba za ta tattauna wannan batu dan samar da matsayar doka, dan nuna matsayin su akan irin wannan matsalar saboda gaba.

Tunda farko shugaban majalisar dokokin jiha, Barista Abdullahi Bawa Wuse ya nemi gwamnatin jiha da hukumar zaben su dakatar da batun zaben har sai bayan kamala shari’ar da ke gaban kotu kan yiwuwar gudanar da zaben, wanda gwamnati da hukumar ke cigaba da shirye-shiryen gudanar da zaben.

Kungiyar jam’iyyun siyasa da ke jihar ( IPAC) bisa jagorancin Hon. Bello Maikujeri ta bayyana gamsuwar takan matsayin hukumar na gudanar da zaben kamar yadda shirye-shiryen ke gudana a halin yanzu.

A wani karin hasken da ya yi wa manema labarai, ya ce sanin kowa ne shugabannin kananan hukumomi na yin shekaru biyu ne a sake zabe, amma saboda sabon dokar da majalisar dokokin jiha suka yi, ya bai wa kananan hukumomi damar wa’adin shekaru uku, yanzu wa’adin su zai kare cikin watan Disamba, ka ga ke dole ne a yi zabe tun da sabon dokar ya ce ba rikon kwarya, in ban da PDP dukkanin jam’iyyun siyasar har APC mai Mulki sun amince da maganar zaben.

Saboda wannan dambarwar da majalisa ke son kawo wa son zuciya kawai amma ba maganar ci gaban dimukuradiyya ba.

Kamar yadda hukumar zaben ta ba mu damar ci gaba da shirye-shirye mafi yawan jam’iyyu sun kammala zaben fidda gwani kuma a shirye muke don fara yakin neman zabe kamar yadda aka tsara.

Wasu rahotanni dai sun tabbatar da cewar gwamnati ta sanya kwamiti don nazartar sabon dokar da kuma yiwuwar yin zaben ko rashin sa.

Tsoron da jama’a ke yi kan zaben yana da nasaba da babban zaben kasa na shekarar 2023 mai da ake zargin idan zaben ya gudana yana iya kara barazana da fargaba a samun babban zaben mai zuwa.

Majalisa
Muhammad Awwal Umar
+ postsBio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.