ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Tsawo

A shekara 2015, Sulemana Abdul Samed ya farka daga barci, amma sai wani abu ya bashi mamaki domin ya lura cewa harshensa ya kara girma har ya cika masa baki ta yadda baya iya yin numfashi sosai.

Bayan ya sha magani da ya sayo a wani kemis, wanda ya rage kumburin harshen, dan makarantar babbar sakandaren bai san cewa wannan lamarin zai sauya rayuwarsa gaba daya ba.

  • Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA
  • An Nemi Fulani Su Manta Da Bambancin Da Ke Tsakaninsu Don Kubuta Daga Matsalar Tsaro

Kuma daga wancan lokacin zuwa yanzu, Sulemana wanda aka fi sani da sunan Awuche- ya rika kara tsawo har sai da ya kai kafa 9.6 kuma ya ci gaba da kara tsawo.

ADVERTISEMENT

“Cikin kowane wata uku zuwa wata hudu na ke kara tsawo. Idan ba ka gan ni cikin wata uku ko hudu ba, za ka na kara tsawo,” in ji Awuche yayin da yake hira da wakilin BBC Pidgin Fabour Nunoo.

Tsawon da Awuche ya yi ya sa ya zama wani shahararre a garinsu Gambaga yayin da mazauna garin daga kananansu har zuwa dattawan garin ke kallonsa da ta’ajibi.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

“Akwai lokacin da wani dan sanda ya ce nazarce shi da tsawona, saboda haka ya ce zai dauki hoto tare da ni,” kamar yadda ya tuna.

Daga ‘yan siyasa zuwa ga jami’an soji da na ‘yansanda duka suna farin ciki da zarar sunga Awuche, wanda baya ga cewa ya fi kowa tsawo, yana kuma da kyawun mu’amala da sauran jama’a.

“Tsawona ya mayar da ni sahahrarre,”kamar yadda ya shaida wa wakilin BBC wanda ya ziyarci garin na Awuche.

Ya kuma ce da a duk lokacin da ya halarci wani biki, sai mutane a wurin su rika matsowa kusa da shi kuma yana son haka sosai.

Ya kan kuma ba su damar daukar hoto da shi a duk lokacin da suka bukaci haka.

“Likitoci sun ce tsawona na lalura ce mai suna ‘gigantism’ Tsawon da Awuche ya yi ba irin wanda aka saba gani ba ne, domin ko likitoci na kiransa da sunan ‘gigantism’ da turancin Ingilishi.

Sun ce wannan matsala ce da kan sa mutum ya yi tsawon da ya zarce na yawancin mutane.

“Yayin da na je asibitin BMC, sai wani mutum farar fata ya ganni kuma sai ya ce ina da lalurar gigantism.

“Ya kuma ce wani likitan da ya rika duba lafiyarsa ya shaida masa cewa akwai wani abu a cikin kwakwalwarsa da ya kamata a yi masa tiyata domin a cire shi.

Ya ce wannan abin ne ke sa kashinsa ke kara girma da tsawo sosai, kuma ya ce idan ba a cire wannan abin daga kwakwalwarsa ba, ba zai daina tsawo ba kuma wannan kai ya shafar lafiyarsa da ingancin walwala da jin dadin rayuwarsa.

Amma duk da haka Awuche yana fatan yin aure da haihuwar ‘ya’ya, wadanda ya ce yake son ganin yadda za su kasance.

Kuma bai damu da cewa ya fi kowa tsawo ba, domin ya ce haka Allah ya so ya gan shi kenan.

Mun ciro muku daga BBC.

Tsawo
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
Next Post
Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

Amurka Da Koriya Ta Kudu Sun Yi Gwajin Makami Don Martani Ga Koriya Ta Arewa

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.