• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sa Kauyukan Sin Samun Ci Gaba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Dalilan Da Suka Sa Kauyukan Sin Samun Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu abokaina ‘yan Najeriya, wadanda suka taba zama a kasar Sin, su kan ambaci yadda zaman rayuwa a cikin biranen Sin ya burge su, yayin da muke hira. Sai dai na kan tunatar da su cewa, ba abun mamaki ba ne, ganin irin saurin ci gaba da aka samu a kauyukan kasar Sin.

Kauyena yana lardin Anhui dake gabashin kasar Sin, wani wuri ne dake cikin duwatsu. Yayin da nake karami, ba na son komawa kauyen tare da iyayena, saboda hanyar ba ta da kyau: a kan kwashe sa’o’i 10 a cikin jirgin kasa, sa’an nan a ci gaba da hawa tarakta har tsawon awa daya.

  • Ka’idar Sin Daya Tilo A Duniya Ke Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan

Ban da wannan kuma, bayan gidan da mutanen kauyen suke amfani da shi ba shi tsabta, hakan yana tsorata ni.

Sai dai zuwa yanzu, kauyen ba kamar yadda yake a baya ba. Jirgin kasa mai saurin gudu ya samar da sauki sosai ga mutanen da suke neman komawa kauyen. Kana mutanen wurin sun gina manyan benaye, ga kuma muhalli mai tsabta da kayatarwa. Ban da haka kuma sun fara yin amfani da dakunan dake cikin gidajensu wajen karbar baki masu yawon shakatawa.

To, me ya sa ake samun ci gaba sosai a kauyukan kasar Sin, cikin gomman shekaru da suka wuce?
Dalili na farko, a ganina, shi ne niyyar gwamnati ta raya kayuka, da yadda take kokarin aiwatar da niyyar.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Babbar manufar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin dake kan karagar mulki a kasar, ita ce kokarin kyautata zaman rayuwar jama’a. Saboda haka gwamnatin kasar ba za ta taba barin ragowar sassan kasar, ko kuma wasu mutane a baya ba, yayin da take kokarin raya tattalin arzikin kasar.

Hakan ya sa gwamnati ta fito da dimbin manufofi wajen raya kauyuka, da kyautata zaman rayuwar manoma. Misali taimakawa kauyuka wajen janyo jari, da samarwa manoma fasahohin zamani na aikin gona, da samar da rance don raya aikin yawon shakatawa a yankin karkara, da dai sauransu.

Dalili na biyu, shi ne yadda wasu matasan kauyuka suka komawa gida, bayan da suka samu ilimi, don taimakawa wajen raya kauyukansu.

A cikin kauyukan da na ziyarta a shekarun baya, na kan ga wasu matasan da suka kammala karatun jami’a a cikin manyan birane, inda suka shafe wasu shekaru suna aiki a can, daga bisani sun koma kauyukansu, sun fara aiki a matsayin jami’ai. Yadda aka wayar musu da kai, ya samar musu da damammakin raya wasu sana’o’i da suka dace da yanayin kauyukan, kana sun fahimci muhimmancin yin amfani da manufofin da gwamnati ta tsara na raya yankunan karkara.

Ban da wannan kuma, dalili na uku shi ne al’adun Sinawa na jure wahalhalu da kokarin aiki.

A kauyukan da na je, na ga wasu tsoffi da yawa da suke gudanar da ayyuka daban daban, misali sayar da kaya, ko kuma nuna fasahohin hannu, har ma wasunsu na tuka manyan motocin tsabtace muhalli. Haka ma dattawa na kokarin aiki, balle ma matasa.

Sinawa suna daukar kokarin aiki a matsayin wata muhimmiyar da’a. Kana nagartattun manufofin gwamnati su ma sun sa mutanen kasar ke da wani tunani na kokarin aiki da samar da hidimomi, don kyautata rayuwarsu, gami da ba da gudunmowa ga ci gaban kasa.

A cikin kauyukan kasar Sin, ana iya ganin yadda mazauna suke da imanin cewar, za su kara jin dadin zaman rayuwarsu a nan gaba. Wannan imani ya tabbatar da cewa, ba za a taba daina kokarin raya kauyukan kasar, da kyautata zaman rayuwar jama’ar wuraren ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Shekara 16 Ya Nutse A Ruwa A Bayelsa 

Next Post

Li Song: Tunanin Cacar Baka Barazana Ne Ga Daidaiton Duniya

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

4 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

5 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

7 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

1 day ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

1 day ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

1 day ago
Next Post
Li Song: Tunanin Cacar Baka Barazana Ne Ga Daidaiton Duniya

Li Song: Tunanin Cacar Baka Barazana Ne Ga Daidaiton Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.