ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sa Kauyukan Sin Samun Ci Gaba

by CMG Hausa
4 years ago
Sin

Wasu abokaina ‘yan Najeriya, wadanda suka taba zama a kasar Sin, su kan ambaci yadda zaman rayuwa a cikin biranen Sin ya burge su, yayin da muke hira. Sai dai na kan tunatar da su cewa, ba abun mamaki ba ne, ganin irin saurin ci gaba da aka samu a kauyukan kasar Sin.

Kauyena yana lardin Anhui dake gabashin kasar Sin, wani wuri ne dake cikin duwatsu. Yayin da nake karami, ba na son komawa kauyen tare da iyayena, saboda hanyar ba ta da kyau: a kan kwashe sa’o’i 10 a cikin jirgin kasa, sa’an nan a ci gaba da hawa tarakta har tsawon awa daya.

  • Ka’idar Sin Daya Tilo A Duniya Ke Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan

Ban da wannan kuma, bayan gidan da mutanen kauyen suke amfani da shi ba shi tsabta, hakan yana tsorata ni.

ADVERTISEMENT

Sai dai zuwa yanzu, kauyen ba kamar yadda yake a baya ba. Jirgin kasa mai saurin gudu ya samar da sauki sosai ga mutanen da suke neman komawa kauyen. Kana mutanen wurin sun gina manyan benaye, ga kuma muhalli mai tsabta da kayatarwa. Ban da haka kuma sun fara yin amfani da dakunan dake cikin gidajensu wajen karbar baki masu yawon shakatawa.

To, me ya sa ake samun ci gaba sosai a kauyukan kasar Sin, cikin gomman shekaru da suka wuce?
Dalili na farko, a ganina, shi ne niyyar gwamnati ta raya kayuka, da yadda take kokarin aiwatar da niyyar.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Babbar manufar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin dake kan karagar mulki a kasar, ita ce kokarin kyautata zaman rayuwar jama’a. Saboda haka gwamnatin kasar ba za ta taba barin ragowar sassan kasar, ko kuma wasu mutane a baya ba, yayin da take kokarin raya tattalin arzikin kasar.

Hakan ya sa gwamnati ta fito da dimbin manufofi wajen raya kauyuka, da kyautata zaman rayuwar manoma. Misali taimakawa kauyuka wajen janyo jari, da samarwa manoma fasahohin zamani na aikin gona, da samar da rance don raya aikin yawon shakatawa a yankin karkara, da dai sauransu.

Dalili na biyu, shi ne yadda wasu matasan kauyuka suka komawa gida, bayan da suka samu ilimi, don taimakawa wajen raya kauyukansu.

A cikin kauyukan da na ziyarta a shekarun baya, na kan ga wasu matasan da suka kammala karatun jami’a a cikin manyan birane, inda suka shafe wasu shekaru suna aiki a can, daga bisani sun koma kauyukansu, sun fara aiki a matsayin jami’ai. Yadda aka wayar musu da kai, ya samar musu da damammakin raya wasu sana’o’i da suka dace da yanayin kauyukan, kana sun fahimci muhimmancin yin amfani da manufofin da gwamnati ta tsara na raya yankunan karkara.

Ban da wannan kuma, dalili na uku shi ne al’adun Sinawa na jure wahalhalu da kokarin aiki.

A kauyukan da na je, na ga wasu tsoffi da yawa da suke gudanar da ayyuka daban daban, misali sayar da kaya, ko kuma nuna fasahohin hannu, har ma wasunsu na tuka manyan motocin tsabtace muhalli. Haka ma dattawa na kokarin aiki, balle ma matasa.

Sinawa suna daukar kokarin aiki a matsayin wata muhimmiyar da’a. Kana nagartattun manufofin gwamnati su ma sun sa mutanen kasar ke da wani tunani na kokarin aiki da samar da hidimomi, don kyautata rayuwarsu, gami da ba da gudunmowa ga ci gaban kasa.

A cikin kauyukan kasar Sin, ana iya ganin yadda mazauna suke da imanin cewar, za su kara jin dadin zaman rayuwarsu a nan gaba. Wannan imani ya tabbatar da cewa, ba za a taba daina kokarin raya kauyukan kasar, da kyautata zaman rayuwar jama’ar wuraren ba. (Bello Wang)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Li Song: Tunanin Cacar Baka Barazana Ne Ga Daidaiton Duniya

Li Song: Tunanin Cacar Baka Barazana Ne Ga Daidaiton Duniya

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.