ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

by Naziru Adam Ibrahim and Sulaiman
10 months ago
Fata

Biyo bayan ƙaddamar da kamfanin sarrafa fata da uwargidan shugaban ƙasa, Remi Tinubu, ta ƙaddamar a Legas, don samar da ayyukan yi ga matasa fiye da dubu goma tare da kawo wa jihar kudin shiga na kusan dala miliyan 250 a duk shekara.

 

Wannan ci gaban ya jawo martani daga Salihu Tanko Yakasai, wanda ya yaba da hangen nesan da jihar Legas ta nuna, amma ya bayyana takaicinsa kan yadda jihohin da ke samar da fata a Arewa, musamman Kano da Sokoto, ba su da irin wannan katafaren kamfani.

ADVERTISEMENT
  • Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
  • NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

A cewarsa, jihohin nan ne suka fi samar da fatar da ake amfani da ita a masana’antu na kasashen Turai irin su Italy da Spain, wadda ake kera takalma da jakunkuna masu tsada da alfarma, inda ya tunatar da cewa tun kafin zuwan Turawa, Kano ta shahara wajen fitar da fata zuwa Morocco, wadda ita kuma take siyarwa ga Turawa.

Ya nuna bacin ra game da cewa duk da kasancewar Kano na da masana’antar gyara fata (tannery), har yanzu ba ta da babbar cibiyar da ke sarrafa fatar zuwa kayayyakin alatu kamar yadda Legas ke ƙoƙarin yi yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

Yakasai ya kawo misalin tattaunawa da aka yi da kamfanoni a kasar China lokacin gwamnatin Abdullahi Ganduje, inda aka kawo tawaga Kano don duba yiyuwar saka hannun jari amma rashin wutar lantarki ya kawo cikas, ganin cewa dokar gwamnatin tarayya a wancan lokaci ta hana jihohi samar da wutar lantarki ta kansu.

Ya bayyana roƙo ga gwamnatin Kano ta yanzu da ta mayar da hankali wajen tabbatar da isasshiyar wutar lantarki, musamman ta hanyar wutar solar ko haɗin gwuiwa da manyan kamfanoni kamar Dangote da BlackRhino, don farfado da masana’antun jihar.

A cewar Yakasai, damuwa mafi girma ita ce yadda albarkatun Arewa ake dauka zuwa wasu jihohin kudu don a sarrafa, daga bisani kuma a dawo da su a sayar wa ’yan Arewa, tsarin da ya ce ya na barin Arewa a matsayin mai samar da kayan albarkatu kawai, yayin da sauran yankuna ke samun ayyukan yi da kuɗaɗen shiga daga sarrafa su.

Wasu matasan Kano a shafukan sada zumunta sun bayyana damuwarsu kan bai wa wasu abubuwa muhimmanci fiye da samar da irin waɗannan kamfanoni da za su gina rayuwar matasa da daƙile ayyukan daba da ya addabi jihar.

Fata
Naziru Adam Ibrahim
+ posts Bio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Gwamnatin Filato Ta Kwato Kadarorin Jihar Da Aka Wawashe
Fata
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna
Labarai

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026
Labarai

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar
Manyan Labarai

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
Next Post
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.