• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shari’ar Musulunci Ba Ta Amince Da Gwajin DNA Don Tabbatar Da Nasaba Ba —Shugabar FIDA

by Mustapha Ibrahim
3 years ago
in Labarai
0
Shari’ar Musulunci Ba Ta Amince Da Gwajin DNA Don Tabbatar Da Nasaba Ba —Shugabar FIDA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabar kungiyar matan lauyoyi (FIDA) ta kasa reshan Jihar Kano, Baristar Bilkisu Ibrahim Sulaiman ta bayyana cewa shari’ar Musulunci na da hanyar tabbatar da nasaba ba ta hanyar kwajin DNA.

Ta ce a cikin takardar da babban magatakardar kotunan daukaka kara ta shari’ar Musulunci da ke Kano, CR Abubakar Haruna Khalid ya gabatar, wanda alkali Isah Idris Makoda ya wakilta, ya tabbatar mana da cewa gwajin jini na kimiyar zamani, da ake yi wanda ake kira DNA, shari’ar Musulunci ba ta aminci da shi ba a mastayin hanyar tabbabar da nasabar jini.

  • Kotu Ta Tsare Hamshakin Dankasuwa Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

Baristar Bilkisu ta bayyana hakan ne a lokacin da take karin haske ga ‘yan jarida bayan bude taron horar da mata lauyoyi na rana daya da Baristar Saidu Tudun Wada ya dauki nauyin wannan horo ga mata lauyoyi kan yadda za su kara fahimtar matsalar warware shari’u da suka shafi aure da saki da neman haki na ciyarwa ko raino a kotuna, bayan an yi sakin aure da sauran matsaloli makamantan wadanan da suke faruna yau da kullom.

Shi ma wakilin CR Abubakar Alkali Isah Idris Makoda, ya ce a kotunan shari’ar Musulunci ba a aiki da gwajin kimiya na jini na DNA a matsayin hanyar tabbatar da nasaban da ga ubansa, domin abu ne na likitoci da suke kira ahlil basari.

Ya ce, “Mu a shari’ar Musulunci da muke aiki da mazahabar Malikiya ba ma aiki da wannan, akwai ayoyi uku a Alkurani da suka fayyace yadda ake gane nasabar da ga ubansa.

Labarai Masu Nasaba

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

“Idan miji ya saki matarsa sai ta haihu bayan wata biyar da kwana 25 ko wata shida, to dansa ne a shari’ance shi ne mafi karancin lokaci da za a danganta da ga ubansa. Haka kuma idan miji ya saki matarsa ta haihu kafin shekara biyar, to dansa ne idan bai zo da shaidar ta yi wani auran ba, wannan shi ne abin da shari’ar Musulunci ta sani amma ba ta yadda gwajin DNA.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kakaki: Kasar Sin Wuri Ne Da Ya Dace Da Zuba Jari

Next Post

An Kaddamar Da Tsarin Biyan Kudi Na Zamani Tsakanin Rwanda Da Sin

Related

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

14 minutes ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

2 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

16 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

19 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

19 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

21 hours ago
Next Post
An Kaddamar Da Tsarin Biyan Kudi Na Zamani Tsakanin Rwanda Da Sin

An Kaddamar Da Tsarin Biyan Kudi Na Zamani Tsakanin Rwanda Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.