ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

by Idris Aliyu Daudawa
9 months ago
Bello

An haifi  Ahmadu Bello a garin Raba ranar   12 ga Yuni 1910. Mahaifinsa, Ibrahim Atiku Bello, shi ne Hakimin kuma ya riƙe muƙamin sarautar  Sarkin Rabah. Yana kuma daga tsatson mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo wanda shi ne asalin masarautar Sakkwato,  babban jika ga Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, kuma jikan Sarkin Musulmi Atiku na Rab.

Ya samu ilimin addinin musulunci tun a gidansu,inda ya koyi Karatun Alkur’ani da kuma Hadisan Manzon Allah Muhammad Sallallahu Alaihis Wasallam. Daganan kuma ya yi makarantar Sakkwato Midil Sukul, da kuma Kwalejin horar da Malamai ta Katsina (wadda yanzu ake kira da suna Kwalejin Barewa). Lokacin da yake ɗan makaranta ana kiransa da  Ahmadu Rabah. Sai dai wasu suna kiransa da Gamji. Ya kammala makarantar a shekarar 1931 daga bisani kuma ya zama Malamin makaranta mai koyar da Turanci a Midil Sukul ta Sakkwato.

  • Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
  • An Gano Karin Gawarwaki 3 Da Jirgin Ruwa Ya Kife Da Fasinjoji 26 A Sokoto

A shekarar 1934 ce aka naɗa, Ahmadu Bello matsayin Hakimin Raba wanda a lokacin Sarkin Musulmi Hassan Dan Mu’azu ya naɗa shi, inda ya gaji ɗanuwansa. A shekarar 1938 kuma sai aka ƙara masa girma,inda ya zama Hakimin Gusau (wato garin da ya zama babban birnin Jihar Zamfara) ya kuma zama ɗan majalisar Sarkin Musulmi a duk shekarar yana da shekara 28. A shekarar 1938, ya yi ƙoƙarin ya zama Sarkin Musulmi  wato Sultan amma bai samu sa’ar cimma burin nasa ba, sai Sarkin Musulmi Siddiƙ Abubakar 111, ya samu sarautar wadda sai da ya yi shekara 50, ya rasu ne a shekarar 1988.

ADVERTISEMENT

Ba tare da ɓata lokaci ba sai sabon Sarkin Musulmin ya naɗa Ahmadu Bello ya bashi Sarautar Sardauna (wadda sarautar Yarima ce) na Sakkwato, sarauta ce ta gargajiya , ya ƙara ma shi girma ya maida shi majalisar ko majalisar gargajiya ta Sakkwato. Waɗannan muƙaman su sauka ba shi dama ta kasancewa mai ba Sarkin Musulmi shawara kan harkokin siyasa.Daga nan kuma  a ba shi muƙamain mai kulawa da Lardin Sakkwato domin ya riƙa kula da Hakimai  47, a shekrar 1944, sai aka sake maido shi fadar ta Sarkin Musulmi a matsayin babban Sakatare na mulkin masarautun gargajiya.

A shekarar 1940 sai ya shiga  Jam’iyyar Mutanen Arewa wadda a ƙarshe ta rikiɗe ta koma Northern People’s Congress (NPC) a shekarar 1951.Amma a shekarar 1948, ya tafi ƙasar Ingila akan tallafin karatu na gwamnati domin ya yi karatu kan lamarin daya shafi ƙananan Hukumomi ta haka ya ƙara koyon yadda ake tafiyar da mulki a gwamnatance.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Bello
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken "Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani"

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.