• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Sa Hannun Gwamnatin Zamfara ‘Yan Daba Suka Farmake Mu – Dan Takarar Gwamna A PDP

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Da Sa Hannun Gwamnatin Zamfara ‘Yan Daba Suka Farmake Mu – Dan Takarar Gwamna A PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar Gwamnan Jihar Zamfara a jam’iyyar PDP, Dakta Dauda Lawal, ya yi tir da harin da wasu ‘yan daba suka kai kan tawagarsa wanda ya yi zargin cewa gwamnatin jihar, ƙarƙashin gwamna Matawalle ce ta ɗauki hayarsu don su aiwatar da hakan.

Ya misalta harin a matsayin kololuwar karya doka da oda tare da neman haifar da hatsaniya da tashin hankali a jihar.

  • Zamfarawa Na Alfahari Da Sadiya Umar Farouq – Gwamna Matawalle

Lawal a wata sanarwar da cibiyar yaɗa labaransa ta fitar a ranar asabar a Gusau, ya ce, wasu ‘yan daba ɗauke da muggan makamai sun kai musu harin ne a daren ranar juma’a a lokacin da suke kan hanyar shiga Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.

Sanarwar ta nuna lamarin a matsayin abin kaico, takaici da damuwa, “An san PDP da mutunta doka da oda, mu jam’iyya ce da muka dukufa wurin gudanar da harkokinmu kan doka da oda. Wannan dalilin ne ma ya sanya sai da muka jira hukumar zaɓe (INEC) ta bada damar gudanar kamfen ɗin gwamna kafin mu shirya wani taron siyasa a jihar Zamfara.

“PDP ta sanya ranar 15 ga watan Oktoba domin ta amshi dubban waɗanda suka sauya sheƙa daga APC zuwa PDP, tare da ƙaddamar da kwamitin yaƙin zaɓen gwamna na 2023.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

“Yan daban da Jam’iyyar APC da Gwamna Matawalle suka ɗauko hayarsu ne suka farmaki tawagarmu a kan hanyarmu ta zuwa Gusau. Motocinmu da dama an lalata, tare da kona wasu a yayin harin.

“A yau kuma ‘yan daban a ƙarƙashin wani Aliyu Alhazai Shinkafi, tsohon Shugaban kwamitin yaki da daba, kuma shugaban hukumar kula da cinkoson ababen hawa (ZAROTA) suka farmaki gidan dan takarar Gwamna na jam’iyyar PDP.

“Wannan sabon harin abun kaico ne inda aka kai hari kan motocin yaƙin zabenmu tare da sace duk wani abu mai muhimmanci a cikinta.

“Mun sani APC da Gwamnatin Matawalle za su iya yin komai domin kawo cikas ga harkokin siyasa da yaƙin zaɓenmu.”

Sanarwar ta bukaci Shugaban ‘yan sanda na ƙasa da sauran hukumomin tsaro da su kaddamar da bincike kan lamarin tare da shigowa cikin batun don kauce wa shigar da jama’a cikin firgici da tashin hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan-Adam Da Ake Iya Sarrafa Shi Daga Nesa

Next Post

An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

22 hours ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

1 day ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

2 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

3 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

6 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

7 days ago
Next Post
An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

An Bude Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.