• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Kaddamar Da Kwamitin Kamfe A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Kaddamar Da Kwamitin Kamfe A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Manjo-Janar Aminu Bande (mai ritaya), ya kaddamar da kwamitin kamfe dinsa a Birnin Kebbi, babban birnin Jihar Kebbi.

Janar Aminu Bande a cikin jawabinsa ya yi alkawarin gudanar da dunkulalliyar gwamnati idan aka zabe shi a zaben 2023 mai zuwa a matsayin gwamnan Jihar kebbi.

  • Ganduje Ya Kaddamar Da Manyan Motocin Sufuri 100 Da Kanana 50 A Kano
  • Wani Harin Bam Ya Yi Sanadin Kashe Aƙalla Mutum 100 A Somaliya

Bande ya ce, “Takararta ba don son rai ba ce, a’a, don ci gaban jihar cikin gaggawa ne.”

Haka kuma ya yi alkawarin yin adalci ga kowace irin al’umma a fadin jihar ba tare da la’akari da addini, kabila da jam’iyya ba da nufin kai jihar ga wani babban mataki da kuma na ci gaba.

Dan takarar ya bukaci ’yan kwamiti yakin neman zaben da su dauki wani sabon salo na yakin neman zabe wanda kowane shugaba da kowane mamba zai kawo da rumfunansa ko rumfarsa na zabe a mazabar da ya ke jefa kuri’a, inda ya kara da cewa duk wanda bai iya kawo rumfar zabensa ba, to bai cancanci zama dan majalisar yakin neman zabensa ba ko yana da wani tasiri ga siyasa ba a yankinsu ko karamar hukumarsu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Kazalika, ya shaida wa taron cewa, “Idan masu rike da madafun iko suka kawo musu kudi su karba, domin naku ne, amma ku tabbatar kun zabe Jam’iyyar PDP domin samun zaman lafiya, ci gaba da kawo canji a jihar Kebbi da Nijeriya baki daya.”

A nasa jawabin shugaban Majalisar yakin neman zaben Gwamnan Jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Shehu-Geda ya yi kira ga ’yan kwamiti da su jajirce da kuma nuna kwazo wajen ganin Jam’iyyar PDP ta lashe dukkan mukamai na zaben 2023 mai zuwa a Jihar kebbi da na shugaban kasa.

Ya bayyana jin dadin yadda dukkan jiga-jigan siyasa a jihar Kebbi sun hallara, don haka ya tabbatar da cewa PDP ta riga ta lashe zabe a Jihar ta Kebbi da yardar Allah.

Kazalika, Shehu-Geda ya nemi goyon baya da hadin kan kowa da kowa domin samun nasarar zabe a fadin jihar.

Alhaji Bala tsohon shugaban jam’iyyar APC a jihar ya ce: “Yanzu na gamsu cewa PDP ta riga ta lashe dukkan mukaman zabe duba da irin manyan da na gani a nan.

“Duk da haka, ina so in roki dukkan ku da ku koma gida ku shawo kan jama’ar ku don su zabi jam’iyyarmu ta PDP a dukkan mukamai na zaben 2023.”

A nasa bangaren kwamishinan hukumar kula da tasrin gurabun daukar aikin gwamnati na tarayya mai wakiltar jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Atiku-Bubu ya bukaci sauran jam’iyyun siyasa da su gudanar da yakin neman zabensu cikin tsafta da kuma limana da kwanciyar hankali batare da wata fitina ba.

Ya ce sun yanke shawarar kafa tanti da PDP ganin yadda tsohon Janar din ya kasance a jam’iyyar ne domin ya kawo hayyaci da kuma canjin da ake so a jihar Kebbi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dan Takarar Gwamnan PDPKebbiKwamitin KamfePDPSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Mutane Da Dama Sun Mutu, Wasu Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Legas 

Next Post

Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma’aikata 

Related

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

17 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

3 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

4 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani

4 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

4 days ago
Next Post
Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma’aikata 

Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma'aikata 

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.