• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya gargaɗi sababbin kwamishinonin zaɓe cewa su nisanci shiga harkokin siyasa ko yin tarayya da ‘yan siyasa, sai fa a bisa ƙa’idar da doka ta tanadar.

 

Yakubu ya bukace su da tabbatar su na bin dukkan tsare-tsaren da dokar zaɓe ko dokar ƙasa ta shimfiɗa wajen gudanar da aikin su.

  • 2023: INEC Ta Samar Da Ingatattun Tsarukan Gudanar Da Tsaftataccen Zabe

Shugaban ya yi wannan gargaɗin ne a lokacin da ya ke rantsar da sababbin Kwamishinonin Zaɓe 19.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Ya ce ya zama tilas su kasance su na aiwatar da komai a bisa ƙa’ida, ba tare da nuƙu-nuƙu ko fifita wani ɓangare ba.

 

Yakubu ya ce: “Kuma a duk lokacin da ku ke ganawa da masu ruwa da tsaki, to ku kasance ba ku wuce ƙa’idar da dokar ƙasa ta gindaya maku.

INEC
Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya na musabiha da sababbin kwamishinonin zaɓen da aka rantsar

“Haka ma a yayin tuntuɓar juna tsakanin ku da jama’a, kada ku tsallake iyakokin da dokar ƙasa ta hana ku tsallakawa.

 

“Sannan ku nisanci kai ziyara ofishin gwamna. Wato ba a son a gan ku gidan gwamnati. Kuma kada su riƙa keɓewa ku na ganawa da ‘yan siyasa ba bisa ƙa’idar aikin ofis ba. Ko bayan tashi daga ofis, ba a yarda su riƙa keɓancewa da ‘yan siyasa ba.

 

“Ku tuna gwamnatin tarayya ku ke wa aiki, saboda haka ita ce abin biyayya a gare ku. Don haka kada ku kauce daga turba, gudun kada ku kai ga zubar da ƙimar ku da darajar INEC.

 

“Kuma ina ƙara jaddada maku cewa hanyar amfani da tsarin tantance sahihiyar rajistar zaɓe ta BVAS ce kaɗai hanyar da aka amince a tantance mai rajistar zaɓe.”

 

Daga cikin sababbin kwamishinonin da Yakubu ya rantsar akwai Uzochukwu Chijoke a Jihar Abiya, Nuru Inusa a Adamawa, Elizabeth Agu a Anambara, Mahmood Nura a Bauchi, Samuel Egu a Binuwai, Yomere Otitsemolebi a Kuros Riba da Onyeka Ugochi a Ebonyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

Next Post

Shin Ko Liverpool Za Ta Iya Kai Bantenta A Bana Kuwa?

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

23 minutes ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

2 hours ago
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

3 hours ago
Labarai

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

5 hours ago
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
Labarai

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

7 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

8 hours ago
Next Post
Shin Ko Liverpool Za Ta Iya Kai Bantenta A Bana Kuwa?

Shin Ko Liverpool Za Ta Iya Kai Bantenta A Bana Kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.