ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Ta Samar Da Ingatattun Tsarukan Gudanar Da Tsaftataccen Zabe

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Yanzu da zaɓen 2023 ke ƙara kusantowa, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa bijiro da wasu ƙwararan matakai huɗu da ta yi sun tabbatar da cewa babu wata hanya da za a iya bi a yi maguɗi anl zaɓen.

Mataki na farko shi ne dabarar tantance wanda ya yi rajistar mallakar katin zaɓe sau biyu ko fiye da haka, wato ‘Biomodal Voter Accreditation System’ (BVAS).

  • Mutum Miliyan 93.5 Ne Za Su Kada Kuri’a A Zaben 2023 – INEC

Na biyu shi ne amfani da na’urar tantance adadin masu zaɓe a rumfunan zaɓe, wato ‘INEC Voter Enrollment Device’ (IVED). Shi wannan tsari ya na maganin masu satar ƙuri’a ko ɓarayin akwatin zaɓe.

ADVERTISEMENT

Na uku shi ne manhajar tattara sakamakon zaɓen da kowa zai iya gani ido-da-ido, wato ‘INEC Result Viewing Portal’ (IRVP).

Da ya ke magana a wurin taron zaburar da matasa muhimmancin zaɓe, wanda ƙungiyar Yiaga Africa ta shirya a Inugu, Mataimakin Sakataren INEC, Injiniya Chidi Nwafor, ya ce Dokar Zaɓe ta 2022 ita ce matakin hana maguɗin zaɓe na huɗu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Saura kwana 116 a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar wakilai da na majalisar dattawa.

Idan ba a manta ba, a farkon Oktoba shi ma Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu, ya tabbatar da cewa maguɗi ba zai yiwu a zaɓen 2023 ba.

A labarin, ya ce INEC ta fito da hanyoyin kashe maguɗin zaɓe.

Yayin da hukumar ke ci gaba da tsare-tsaren gudanar da zaɓubbukan 2023, shugaban ya bugi ƙirji da cewa INEC ta samu nasarar toshe duk wata ƙofar da za a iya bi a yi maguɗi.

Da ya ke jawabi a wani taron da aka shirya a Cocin St. James na Ɗariƙar Angalika da ke Asokoro, Abuja, a kwanan baya, Yakubu ya ce INEC ta samu wannan gagarumar nasara ne ta hanyar ƙirƙiro tsarin tantance mai rajistar zaɓe na ƙeƙe-da-ƙeƙe, wato BVAS.

Yakubu, wanda Mataimakin Kakakin Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ba hukumar, Chukwuemeka Ugboaja, ya wakilta, ya tsarin tantance mai karin rajistar hikima ce da basirar injiniyoin INEC ta kai su ga kirƙiro shi.

Ya ce BVAS zai ƙara wa INEC ƙarfin gwiwar tabbatar da cewa ta shirya zaɓe sahihi, wanda babu yadda za a iya yin maguɗi a lokacin zaɓe.

Ya ce: “Abu na biyu da zai ƙara wa zaɓen 2023 inganci shi ne sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022. Sashe na 9 (6) ya bai wa INEC ikon daina yi wa mutane rajista kwanaki 90 kafin zaɓe. Daga nan ne kuma sai hukumar ta tankaɗe tare da tace rajistar ɗungurugum.

“Kuma mutane su fahimci cewa INEC ba ta iya soke rajistar kowa. Amma ta na da ikon soke rajistar wanda ya yi rajista sau biyu.

“Hanya ta uku da za a kawo ƙarshen maguɗin zaɓe ita ce aikawa da sakamakon zaɓe kai-tsaye ta na’urorin kafafen sadarwa na zamani daga rumfar zaɓe.

“Sannan kuma Sashe na 51 na Dokar Zaɓe ta 2021 ya nuna ƙin amincewa da sakamakon zaɓen inda adadin ƙuri’un da aka jefa a akwati su ka haura adadin yawan waɗanda aka tantance ta tsarin BVAS.

“Sannan kuma a zaɓen 2023, Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2023 ta haramta wa INEC karɓar sakamakon da aka tilasta wa jami’in zaɓe bayyana sakamkon zaɓe.”

Ya buga misali da zaɓen sanata na Jihar Imo a 2019, wanda duk da cewa tilasta jami’in INEC aka yi ya karanta sakamakon zaɓen, amma kotu ta amince da sakamakon. Ya ce a yanzu ƙarƙashin sabuwar dokar zaɓe, hakan ba zai yiwu ba.

Daga ƙarshe ya yi kira ga manya da masu ilimi mazauna birane cewa su daure su riƙa fita su na jefa ƙuri’a a ranar zaɓe.

Ya nuna damuwa kan cewa mazauna birane, musamman masu hali da manyan ‘yan boko, ba su zuwa su na jefa ƙuri’a, duk kuwa da cewa sun san muhimmancin yin zaɓen.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
PDP Ta Maka APC A Kotu, Ta Nemi A Kori Shugaban APC Na Kasa Daga Mukaminsa

PDP Ta Maka APC A Kotu, Ta Nemi A Kori Shugaban APC Na Kasa Daga Mukaminsa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.