• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ma’aikata 3 Sun Lakada Wa Babban Alkalin Kotun Majistare Duka A Jihar Kebbi

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Wasu Ma’aikata 3 Sun Lakada Wa Babban Alkalin Kotun Majistare Duka A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gurfanar da wasu mutane uku a gaban kotun Majistare ta daya da ke zamanta a Birnin Kebbi bisa zarginsu da cin zarafin babban Alkalin kotun majistare Umar Salihu Kokani ta hanyar lakada masa dukan tsiya.

Mutanen uku da ake tuhumar su ne Aliyu Shehu Jega, Yahaya Badare da kuma Surajo Shehu sannan dukkansu ma’aikatan ne a ma’aikatar ilimi mai zurfi ta jihar Kebbi.

  • Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi

A karar da aka shigar da su mai lamba BK/358c’/2022 akan laifukan hada baki, karya, cin zarafi da bata suna wanda ya saba wa sashi na 373 na kundin Final kod ta jihar Kebbi na shekarar 2021.

Yayin da ya ke gurfanar da wadanda ake tuhumar, dan sanda mai shigar da kara, Insifekta Jibril Abba, ya shaida wa kotun cewa, wadanda ake tuhuma ukun ma’aikatan ma’aikatar ilimi mai zurfi ne ta jihar Kebbi, kuma sun kai wa babban Alkali Kotun majastare Umar Salihu Kokani hari a lokacin da ya ke alwala a masallacin.

Ya shaida wa Kotun cewa, a shirye suke su bude karar nasu, amma saboda rashin halartar babban shaida, za su nemi a dage sauraron karar zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022 don ci gaba da sauraren karar gadan-gadan.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Hakazalika, wadanda ake tuhumar ba su samu wakilcin wani Lauya a gaban kotun ba

Alkalin kotun, Majistare Hassan Kwaido, ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022 domin ci gaba da sauraron karar.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan dage shari’ar, Lauyan majastare Umar Salihu Kokani, Barista Sani Dan-Yaro Majidadi, ya bayyana cewa “Abin da suke so shi ne adalci ga wanda aka ci zarafinsa wanda shi ne Babban Alkalin Kotun majastare ta UKu da ke Birnin Kebbi.”

“Bugu da kari, Barista Majidadi ya yi mamaki, idan wani zai iya kai wa Babban Majistare hari ba tare da wani sakamako ba, zai aika da sigina mara kyau ga jama’a a cikin al’umma cewa za a iya cin zarafin kowa batare da doka ta yi aiki a kansu ko kanta, inji Barista Sani Dan-yaro”.

“Abin da muke so shi ne adalci, ba ma son halin da mutane za su rika daukar doka a hannunsu suna ganin cewa, babu abin da zai faru, a wasu lokutan ma wasu da ake zargin sun kashe wani Majistare a Jihar Kebbi, har ya zuwa yanzu, babu wani abu da aka yi balle mu yi tunanin wani adalci.

“Don haka, muna son lamarin ya canza, don kada mutane su rika daukar doka a hannunsu kuma su kuskura cewa ba za a samu sakamako ba,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanonin Kasar Sin Sun Gina Layin Dogo Da Ya Haura Tsawon Kilomita 10,000 A Sassan Nahiyar Afirka

Next Post

El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

45 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.