ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ma’aikata 3 Sun Lakada Wa Babban Alkalin Kotun Majistare Duka A Jihar Kebbi

by Sulaiman and Umar Faruk
4 years ago
Kebbi

An gurfanar da wasu mutane uku a gaban kotun Majistare ta daya da ke zamanta a Birnin Kebbi bisa zarginsu da cin zarafin babban Alkalin kotun majistare Umar Salihu Kokani ta hanyar lakada masa dukan tsiya.

Mutanen uku da ake tuhumar su ne Aliyu Shehu Jega, Yahaya Badare da kuma Surajo Shehu sannan dukkansu ma’aikatan ne a ma’aikatar ilimi mai zurfi ta jihar Kebbi.

  • Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi

A karar da aka shigar da su mai lamba BK/358c’/2022 akan laifukan hada baki, karya, cin zarafi da bata suna wanda ya saba wa sashi na 373 na kundin Final kod ta jihar Kebbi na shekarar 2021.

ADVERTISEMENT

Yayin da ya ke gurfanar da wadanda ake tuhumar, dan sanda mai shigar da kara, Insifekta Jibril Abba, ya shaida wa kotun cewa, wadanda ake tuhuma ukun ma’aikatan ma’aikatar ilimi mai zurfi ne ta jihar Kebbi, kuma sun kai wa babban Alkali Kotun majastare Umar Salihu Kokani hari a lokacin da ya ke alwala a masallacin.

Ya shaida wa Kotun cewa, a shirye suke su bude karar nasu, amma saboda rashin halartar babban shaida, za su nemi a dage sauraron karar zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022 don ci gaba da sauraren karar gadan-gadan.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

Hakazalika, wadanda ake tuhumar ba su samu wakilcin wani Lauya a gaban kotun ba

Alkalin kotun, Majistare Hassan Kwaido, ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022 domin ci gaba da sauraron karar.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan dage shari’ar, Lauyan majastare Umar Salihu Kokani, Barista Sani Dan-Yaro Majidadi, ya bayyana cewa “Abin da suke so shi ne adalci ga wanda aka ci zarafinsa wanda shi ne Babban Alkalin Kotun majastare ta UKu da ke Birnin Kebbi.”

“Bugu da kari, Barista Majidadi ya yi mamaki, idan wani zai iya kai wa Babban Majistare hari ba tare da wani sakamako ba, zai aika da sigina mara kyau ga jama’a a cikin al’umma cewa za a iya cin zarafin kowa batare da doka ta yi aiki a kansu ko kanta, inji Barista Sani Dan-yaro”.

“Abin da muke so shi ne adalci, ba ma son halin da mutane za su rika daukar doka a hannunsu suna ganin cewa, babu abin da zai faru, a wasu lokutan ma wasu da ake zargin sun kashe wani Majistare a Jihar Kebbi, har ya zuwa yanzu, babu wani abu da aka yi balle mu yi tunanin wani adalci.

“Don haka, muna son lamarin ya canza, don kada mutane su rika daukar doka a hannunsu kuma su kuskura cewa ba za a samu sakamako ba,” in ji shi.

Kebbi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe
  • Sulaiman
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
  • Sulaiman
    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
  • Sulaiman
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
Kebbi
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.