ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ma’aikata 3 Sun Lakada Wa Babban Alkalin Kotun Majistare Duka A Jihar Kebbi

by Sulaiman and Umar Faruk
4 years ago
Kebbi

An gurfanar da wasu mutane uku a gaban kotun Majistare ta daya da ke zamanta a Birnin Kebbi bisa zarginsu da cin zarafin babban Alkalin kotun majistare Umar Salihu Kokani ta hanyar lakada masa dukan tsiya.

Mutanen uku da ake tuhumar su ne Aliyu Shehu Jega, Yahaya Badare da kuma Surajo Shehu sannan dukkansu ma’aikatan ne a ma’aikatar ilimi mai zurfi ta jihar Kebbi.

  • Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi

A karar da aka shigar da su mai lamba BK/358c’/2022 akan laifukan hada baki, karya, cin zarafi da bata suna wanda ya saba wa sashi na 373 na kundin Final kod ta jihar Kebbi na shekarar 2021.

ADVERTISEMENT

Yayin da ya ke gurfanar da wadanda ake tuhumar, dan sanda mai shigar da kara, Insifekta Jibril Abba, ya shaida wa kotun cewa, wadanda ake tuhuma ukun ma’aikatan ma’aikatar ilimi mai zurfi ne ta jihar Kebbi, kuma sun kai wa babban Alkali Kotun majastare Umar Salihu Kokani hari a lokacin da ya ke alwala a masallacin.

Ya shaida wa Kotun cewa, a shirye suke su bude karar nasu, amma saboda rashin halartar babban shaida, za su nemi a dage sauraron karar zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022 don ci gaba da sauraren karar gadan-gadan.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Hakazalika, wadanda ake tuhumar ba su samu wakilcin wani Lauya a gaban kotun ba

Alkalin kotun, Majistare Hassan Kwaido, ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022 domin ci gaba da sauraron karar.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan dage shari’ar, Lauyan majastare Umar Salihu Kokani, Barista Sani Dan-Yaro Majidadi, ya bayyana cewa “Abin da suke so shi ne adalci ga wanda aka ci zarafinsa wanda shi ne Babban Alkalin Kotun majastare ta UKu da ke Birnin Kebbi.”

“Bugu da kari, Barista Majidadi ya yi mamaki, idan wani zai iya kai wa Babban Majistare hari ba tare da wani sakamako ba, zai aika da sigina mara kyau ga jama’a a cikin al’umma cewa za a iya cin zarafin kowa batare da doka ta yi aiki a kansu ko kanta, inji Barista Sani Dan-yaro”.

“Abin da muke so shi ne adalci, ba ma son halin da mutane za su rika daukar doka a hannunsu suna ganin cewa, babu abin da zai faru, a wasu lokutan ma wasu da ake zargin sun kashe wani Majistare a Jihar Kebbi, har ya zuwa yanzu, babu wani abu da aka yi balle mu yi tunanin wani adalci.

“Don haka, muna son lamarin ya canza, don kada mutane su rika daukar doka a hannunsu kuma su kuskura cewa ba za a samu sakamako ba,” in ji shi.

Kebbi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Kebbi
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Next Post
El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.