• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Labarai
0
ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC ta fara binciken tabbatar da matsayin aiwatar da ayyuka a Mazabun Majalisar Tarayya 10 wadanda Gwamnatin Tarayya ta bayar da kwangilar aiwatar da su kan sama da naira miliyan 355 a Sakkwato.

Binciken gano matsayin ayyukan yana a karkashin rukuni na biyar na bankado ayyukan Mazabun Tarayya da Hukumar ICPC ke aiwatarwa a Jihohi 21 wadanda aka bayar da aikin su a cikin Kasafin Kudin 2021.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da ‘Yan Tawagar Biki 50 A Hanyar Zamfara Zuwa Sokoto

Jagoran tagagar Hukumar ICPC Mista Sa’idu Yahaya ya bayyanawa manema labarai a yau cewar za su gudanar da binciken ayyuka a yankin Majalisar Dattawa biyu da Mazabun ‘Yan Majalisar Tarayya biyar. Daga ciki akwai Mazabar Sakkwato ta Arewa wadda Sanata Aliyu Wamakko, Mataimakin Shugaban Kwamitin Yaki da Rashawa a Majalisar Dattawa ke wakilta.

“An bayar da kwangilar ayyukan a kan naira miliyan 355, 391, 657. 95 tare da tsammanin za a kammala su bakidaya. Tawagar mu ta kunshi wakilan ICPC, kungiyoyin farar hula da ‘yan jarida wadanda duka za su bi diddigin ayyukan.”

“Hakan na da manufar gano ayyukan, yanayin ayyukan da adadin kudin da aka kashe a ayyukan da adadin kudin kwangila, ‘yan kwangila, kudaden da aka biya da gano mutanen da suka jagoranci ayyukan.” Ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

A cewarsa tawagar za ta kuma binciko kamfunan da suka yi ayyukan, binciken ko an cika sharuddan ayyukan da kudaden haraji. Ya ce za su duba kima da muhimmancin ayyukan ga al’ummar da aka yi domin su.

Ayyukan da za a gudanar da binciken gano su sun hada da samar da motoci a yankin Majalisar Dattawa a Sakkwato ta Gabas da Sanata Ibrahim Abdullahi Gobir ke wakilta da babura a Mazabar Sakkwato ta Arewa da Sanata Aliyu Wamakko, tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato ke wakilta.

Haka ma akwai binciken gano tabbatar da rarraba babura 188 a Mazabar Gwadabawa/Illela da Hon. Abdullahi Salame ke wakilta a Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da samar da takin zamani na NPK da fanfunan ruwa a Mazabar Kware/Wamakko da shirin karfafawa al’umma kan aikin gona a Mazabar Tarayya ta Bodinga/Dange/Shuni/Tureta wadda Hon. Balarabe Kakale ke wakilta a wa’adin zango na farko.

Tawagar ta riga ta ziyarci wasu daga cikin ayyukan da aka aiwatar a Mazabar Tarayya ta Sakkwato ta Arewa/Sakkwato ta Kudu da Bodinga/Dange/Shuni/Tureta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Next Post

Gwamnatin APC Ta Yaudari ‘Yan Nijeriya – Kwankwaso

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

50 minutes ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

2 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

3 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

5 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

7 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

11 hours ago
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Gwamnatin APC Ta Yaudari 'Yan Nijeriya - Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.