• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Gamsu Da Manufofin Kwankwaso – Matasan Arewa A Legas

by yahuzajere
3 years ago
in Siyasa
0
Abin Da Ya Sa Muka Gamsu Da Manufofin Kwankwaso – Matasan Arewa A Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Matasan Arewa Mazauna Jihar Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya bayyana cewa sun gamsu da manufofin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bisa yadda suka ƙunshi dabarun magance manyan matsalolin da suka addabi Nijeriya a zamanin nan.

A cewar Galadanci, lokaci ya yi da ‘Yan Nijeriya za su zabura su tabbatar da nagarta wajen zaɓen shugabannin da suka fi cancanta a zaɓen 2023 domin fita daga halin da suke ciki na rashin tsaro da tsadar rayuwa.

  • Shugaba Buhari Ya Gana Da Sarki Charles III Na Birtaniya A Landon

Ya ƙara da cewa, “Ƙungiyarmu ta Gamayyar Matasan Arewa a Legas, mun fahimci manufofin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Dr Rabi’u Musa Kwankwaso kuma mun gamsu da jawabinsa da ya yi wa al’ummar Nijeriya da ma duniya baki ɗaya. Abin da ya fi ɗaukar hankalinmu a jawabin nasa shi ne idan Allah ya ba su ikon cin nasara a zaɓen 2023, ya ƙudiri aniyar magance matsalolin tsaron cikin gida a Nijeriya da iyyakokinta, musamman ƙudirin da ya yi na zai ɗauki sojoji kimanin miliyan ɗaya da ‘yansanda miliyan ɗaya da sauran jami’an tsaro waɗanda za a tantance su tun daga matakin ƙaramar hukumarsu har zuwa jiha, yin hakan babbar nasara ce ga ƙasarmu da kuma ‘yan ƙasa baki ɗaya. Sannan da batun bunƙasa harkar ilimi da sauran tsare-tsare na alheri wanda waɗannan maganganu su ne suka ba mu damar mu taya su da addu’o’inmu na alheri a kan Allah ya cika musu burinsu mu samu zaman lafiya da ci gaban al’umma.

“Ƙasarmu mun san yadda Allah ya yi mata arzikin ma’adanai masu daraja waɗanda muna ji muna gani wasu na yi mana kisan gillah, suna amfani da wannan damar suna kwasar dukiyar. Sun haɗa baki da baƙin haure an hana mu zaman lafiya. Don haka wannan lokaci ne da za mu mu fito domin ganin an daina yi wa al’ummar Nijeriya wasan wawaso da dukiyar da Allah ya bayar ga ƙasar domin al’ummar Nijeriya su amfana. Ba kuɗi za a ba mu ba domin muna dimokraɗiyya ne a yanzu, ya kamata mu tashi tsaye mu kawo wa ƙasarmu ci gaban da za mu yi alfari da ita a matsayin Nijeriya ƙasa ɗaya mai al’umma ɗaya da ke samun bunƙasa.

“Muna kira ga ‘Yan Nijeriya a kan su fahimci cewa abin da muka fi buƙata a wannan zaɓen na 2023 da za a yi shi ne mu yi watsi da harkar ubangida, kowane ubangida yana da wani muradin kansa a fagen siyasa kuma wannan muradin ba don kishin ci gaban jama’a ba ne sai dai ci gaban kansa da iyalansa. Don haka wannan ne lokaci mafi dacewa da za mu yaƙi azzalimai waɗanda ana yi mana kisan gillah ba dare ba rana amma ba su damu ba, yadda za su ci gaba da mulki da ɗora nasu a kai kawai suke ƙoƙarin yi saboda sun mayar da mulkin ƙasar ya zama na gado.” In ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

Ya ƙara da cewa, yadda aka riƙa sayen wakilai masu zaɓe tun daga zaɓen fitar da gwani, manuniya ce ta neman ƙara danne talakan Nijeriya.

“A idon duniya manyan ‘yan takara suka dinga sayen wakilai masu zaɓe da ake ce wa ‘delegate’ domin su ci gaba da kassara mu. Talakan Nijeriya ya san irin uƙubar da yake ciki. Don haka muna ƙara yin kira ga shugabannin manyan ƙasashe na duniya, matuƙar suna son ɗorewar dimokuraɗiyya a Nijeriya, su taimaka wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ne suka zaɓi waɗanda suka cancanta da za su fitar da su daga halin da ƙasar take ciki. Duk wani ɗan ƙasa nagari da ka sani ya gaji da kisan gilla da tsadar rayuwa. Mu a matsayinmu na gamayyar matasan arewa da ke Legas, muna kira ga dukkan ‘yan ƙasa ba tare da bambancin ƙabila ko addini ba, mu tashi tsaye mu zaɓi cancanta, wannan ne kaɗai zai kai mu ga tudun mun tsira a 2023.” Ya bayyana.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ASUU: Ndume Ya Bukaci A Zabtare Albashin ‘Yan Majalisa Kashi 50 Cikin 100 A Biya Malaman Jami’a

Next Post

Rikicin Doguwa Da Garo: Yadda Siyasar Kano Ta Dauki Sabon Salo

Related

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

47 minutes ago
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Siyasa

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

5 hours ago
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Siyasa

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

8 hours ago
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

2 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

2 days ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

2 days ago
Next Post
A Shirye Kwankwaso Yake Ya Karbi Alasan Ado Doguwa A Kwankwasiyya —Rurum

Rikicin Doguwa Da Garo: Yadda Siyasar Kano Ta Dauki Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.