ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Muka Gamsu Da Manufofin Kwankwaso – Matasan Arewa A Legas

by yahuzajere
4 years ago
Kwankwaso

Shugaban Gamayyar Matasan Arewa Mazauna Jihar Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya bayyana cewa sun gamsu da manufofin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bisa yadda suka ƙunshi dabarun magance manyan matsalolin da suka addabi Nijeriya a zamanin nan.

A cewar Galadanci, lokaci ya yi da ‘Yan Nijeriya za su zabura su tabbatar da nagarta wajen zaɓen shugabannin da suka fi cancanta a zaɓen 2023 domin fita daga halin da suke ciki na rashin tsaro da tsadar rayuwa.

  • Shugaba Buhari Ya Gana Da Sarki Charles III Na Birtaniya A Landon

Ya ƙara da cewa, “Ƙungiyarmu ta Gamayyar Matasan Arewa a Legas, mun fahimci manufofin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Dr Rabi’u Musa Kwankwaso kuma mun gamsu da jawabinsa da ya yi wa al’ummar Nijeriya da ma duniya baki ɗaya. Abin da ya fi ɗaukar hankalinmu a jawabin nasa shi ne idan Allah ya ba su ikon cin nasara a zaɓen 2023, ya ƙudiri aniyar magance matsalolin tsaron cikin gida a Nijeriya da iyyakokinta, musamman ƙudirin da ya yi na zai ɗauki sojoji kimanin miliyan ɗaya da ‘yansanda miliyan ɗaya da sauran jami’an tsaro waɗanda za a tantance su tun daga matakin ƙaramar hukumarsu har zuwa jiha, yin hakan babbar nasara ce ga ƙasarmu da kuma ‘yan ƙasa baki ɗaya. Sannan da batun bunƙasa harkar ilimi da sauran tsare-tsare na alheri wanda waɗannan maganganu su ne suka ba mu damar mu taya su da addu’o’inmu na alheri a kan Allah ya cika musu burinsu mu samu zaman lafiya da ci gaban al’umma.

ADVERTISEMENT

“Ƙasarmu mun san yadda Allah ya yi mata arzikin ma’adanai masu daraja waɗanda muna ji muna gani wasu na yi mana kisan gillah, suna amfani da wannan damar suna kwasar dukiyar. Sun haɗa baki da baƙin haure an hana mu zaman lafiya. Don haka wannan lokaci ne da za mu mu fito domin ganin an daina yi wa al’ummar Nijeriya wasan wawaso da dukiyar da Allah ya bayar ga ƙasar domin al’ummar Nijeriya su amfana. Ba kuɗi za a ba mu ba domin muna dimokraɗiyya ne a yanzu, ya kamata mu tashi tsaye mu kawo wa ƙasarmu ci gaban da za mu yi alfari da ita a matsayin Nijeriya ƙasa ɗaya mai al’umma ɗaya da ke samun bunƙasa.

“Muna kira ga ‘Yan Nijeriya a kan su fahimci cewa abin da muka fi buƙata a wannan zaɓen na 2023 da za a yi shi ne mu yi watsi da harkar ubangida, kowane ubangida yana da wani muradin kansa a fagen siyasa kuma wannan muradin ba don kishin ci gaban jama’a ba ne sai dai ci gaban kansa da iyalansa. Don haka wannan ne lokaci mafi dacewa da za mu yaƙi azzalimai waɗanda ana yi mana kisan gillah ba dare ba rana amma ba su damu ba, yadda za su ci gaba da mulki da ɗora nasu a kai kawai suke ƙoƙarin yi saboda sun mayar da mulkin ƙasar ya zama na gado.” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Ya ƙara da cewa, yadda aka riƙa sayen wakilai masu zaɓe tun daga zaɓen fitar da gwani, manuniya ce ta neman ƙara danne talakan Nijeriya.

“A idon duniya manyan ‘yan takara suka dinga sayen wakilai masu zaɓe da ake ce wa ‘delegate’ domin su ci gaba da kassara mu. Talakan Nijeriya ya san irin uƙubar da yake ciki. Don haka muna ƙara yin kira ga shugabannin manyan ƙasashe na duniya, matuƙar suna son ɗorewar dimokuraɗiyya a Nijeriya, su taimaka wajen tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ne suka zaɓi waɗanda suka cancanta da za su fitar da su daga halin da ƙasar take ciki. Duk wani ɗan ƙasa nagari da ka sani ya gaji da kisan gilla da tsadar rayuwa. Mu a matsayinmu na gamayyar matasan arewa da ke Legas, muna kira ga dukkan ‘yan ƙasa ba tare da bambancin ƙabila ko addini ba, mu tashi tsaye mu zaɓi cancanta, wannan ne kaɗai zai kai mu ga tudun mun tsira a 2023.” Ya bayyana.

 

Kwankwaso
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
A Shirye Kwankwaso Yake Ya Karbi Alasan Ado Doguwa A Kwankwasiyya —Rurum

Rikicin Doguwa Da Garo: Yadda Siyasar Kano Ta Dauki Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.