• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

by Sulaiman
3 years ago
Ortom

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana kalaman da gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom ya yi a matsayin ‘masu tsauri’, wanda a lokacin da yake yin Allah wadai da kisan mutane 18 da aka yi a yankin karamar hukumarsa a ranar Juma’ar da ta gabata ya ce ba zai taba goyon bayan wani Bafulatani ya sake zama shugaban kasar Najeriya.

 

Ortom ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar bakuncin takwarorinsa na jihohin Rivers, Oyo, Abia da Enugu a wani liyafar cin abinci a Makurdi, ya ce: “Kuna so in zama bawa ga Bafulatani. Gara in mutu. Ana kashe mutanena kuna so in yi shiru. Ba zan taba goyon bayan Bafulatani ya zama shugaban kasa ba. Idan kuma akwai wani wanda yake shirye ya yi aiki tare da ni don tabbatar da tsaron jama’ata, zan yi aiki da shi.”

  • Abin Da Ya Sa Muka Gamsu Da Manufofin Kwankwaso – Matasan Arewa A Legas

Sai dai kungiyar dattawan Arewa a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba mai dauke da sa hannun Daraktan yada labarai da fa’ida, Dakta Hakeem Baba-Ahmed, ta ce kalaman Gwamnan kwata-kwata bai dace da shugaba ba, musamman a daidai lokacin da ake siyasantar da matsalar rashin tsaro a kasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Kungiyar ta ce, “mu ma kamar sauran ‘yan Najeriya, mun kalli bidiyon da Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom ke magana a cikin yanayi da kuma yare da bai dace da shugaba ba.

 

“Kungiyar Dattawan Arewa ta ci gaba da yin Allah-wadai da yanayin kawanya da rashin tsaro da ‘yan Nijeriya suka yi rayuwa a ƙarƙashinsu a cikin ‘yan shekarun nan. Musamman a Arewa ‘yan damfara fulani sun yi fice a matsayin masu kisa da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

 

“Ya kamata gwamna Ortom ya cika rantsuwar da ya yi da kuma alkawarin da ya yi na yin rayuwa a matsayinsa na shugaban al’ummarsa.

 

“Ya kamata ya guje wa sha’awar buga wasan kwaikwayo wanda, kamar sauran ‘yan Najeriya, ke da burin samun sauki da kuma kawo karshen kashe-kashen da ke tayar da juna da kuma kai su ga rikice-rikice marasa iyaka.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.