• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Buni Ya Gabatar Da Biliyan 163 A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
Buni

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya gabatar wa zauren majalisar dokokin Jihar Yobe kudurin kasafin kudin 2023 na kimanin N163,155,366,000, domin amincewa. 

Da yake gabatar da kasafin kudin wannan shekara a ranar Alhamis, wanda aka yi wa taken: “Kasafin kudi domin ci gaba daga inda aka tsaya, karfafawa tare da sauya fasalin tattalin arziki” ga zauren majalisar dokokin jihar, Gwamna Buni, ya ce an yi kiyasin kasafin ne domin karfafa nasarorin da ya samu a baya wajen ciyar da jihar gaba.

  • El-rufai Ya Amince Da Nadin Wazirin Garin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Masarautar Jere
  • Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023

Kasafin kudin 2023 ya ragu da kashi 0.49 cikin 100, idan aka kwatanta da na shekarar 2022 da ta gabata.

Yayin da a cikin kasafin aka ware N87,800,717,000 wajen gudanar da ayyukan gwamnati na yau da kullum, kimanin kaso 57 cikin 100 na adadin kasafin kudin.

Bugu da kari kuma Gwamna Buni, ya bayyana cewa, an ware jimillar N75,354,649,00 a bangaren manyan ayyukan da gwamnatin jihar za ta aiwatar a wannan shekarar, wanda ya tsaya madadin kaso 43 cikin 100 na kasafin kudin.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Ya kara da cewa kasafin kudin zai karkata ne wajen kammala ayyukan da ake ci gaba da aiwatarwa domin cimma muradun gwamnati wajen farfado da yankunan da rikicin Boko Haram ya tagayyara a jihar, bunkasa harkokin ci gaba da inganta tattalin arziki da walwalar jama’ar jihar.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da kokarin da ta ke wajen gina tituna, da farfado da fannin ilimi da kuma kudirin kammala sauran cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko, a karkashin kudurin gwamnatin jihar na kafa cibiyar kiwon lafiya a matakin farko guda daya a cikin kowace gunduma daga cikin gundumomi 178 a fadin Jihar Yobe.

A nashi bangare, kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe, Ahmed Mirwa, ya bayar da tabbacin aiki tukuru wajen ganin zauren majalisar ya duba kasafin kudin tare da amincewa da shi domin bai wa bangaren zartaswa damar gudanarwa da al’ummar Jihar Yobe ayyukan ci gaba, wadanda suke kunshe a cikin kasafin kudin na 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro
Labarai

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Next Post
Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Hukumar EFCC Ta Tsare Wasu Jami’anta 10 Bisa Zargin Karkatar Da Kayan Aiki

EFCC Ta Ƙwato Kadarorin Naira Biliyan 500 A Ƙarƙashin Gwamnatin Tinubu – Shettima

October 20, 2025
Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.