• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwari 4 Na Kasar Sin Za su Taimaka Wajen Samar Da Sabon Abun Al’ajabi A Asiya Da Yankin Tekun Pasifik

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarwari 4 Na Kasar Sin Za su Taimaka Wajen Samar Da Sabon Abun Al’ajabi A Asiya Da Yankin Tekun Pasifik
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 18 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping na kasar Sin ya bayyana cikin jawabinsa a yayin kwarya-kwaryar taron shugabanni mambobin kungiyar hadin kan tattalin arziki ta Asiya da yankin tekun Pasifik APEC karo na 29 cewa, yanzu duniya ta sake shiga muhimmin lokaci a tarihi.

Asiya da yankin tekun Pasifik suna kara taka muhimmiyar rawa, yayin da matsayinsu ya samu ingantuwa sosai.

  • Kasashen Tsibiran Tekun Pasifik Sun Fi Bukatar Sahihiyar Gudummawa Daga Kasar Amurka

A cikin jawabinsa, Xi Jinping ya gabatar da shawarwari guda 4 kan yadda za a hada hannu wajen raya makomar bai daya a Asiya da yankin tekun Pasifik a sabon halin da ake ciki, wato kiyaye adalci a duniya, a kokarin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Asiya da yankin tekun Pasifik, da tsayawa kan bude kofa ga ketare da dunkule dukkan bangarori, a kokarin raya Asiya da yankin tekun Pasifik mai wadata, da nacewa kan raya Asiya da yankin tekun Pasifik mai tsabta da kyan gani ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma tsayawa kan taimakawa juna a Asiya da yankin tekun Pasifik, wadanda ke da makoma iri daya.

Ruhin wadannan shawarwari 4 sun yi daidai da shawarwari guda 6 da Xi Jinping ya ambato cikin rubutaccen jawabinsa a yayin taron shugabannin masana’antu da kasuwanci na kungiyar APEC a ranar 17 ga wata.

Dukkansu sun takaita fasahohin da aka samu wajen samar da abun al’ajabi na Asiya da yankin tekun Pasifik, sun kuma tsara manyan tsare-tsare kan halin da ake ciki yanzu. Shawarwarin na da ma’ana mai zurfi kan hakikanin halin da ake ciki.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Ba za a samu ci gaba ba, sai an samu zaman lafiya tukuna. Kana kuma, ci gaba ya na ba da tabbaci wajen samun zaman lafiya.

A matsayinta na muhimmiyar mambar kungiyar APEC, kasar Sin ta samu ci gaba sakamakon kasancewa a Asiya da yankin tekun Pasifik, yayin da ta ba da nata gudummowa wajen raya Asiya da yankin tekun Pasifik.

Ya zuwa shekarar 2020, jimillar yawan cinikin da ke tsakanin Sin da mambobin kungiyar APEC ta kai dalar Amurka triliyan 2.87. Kwanan baya, an samu nasarar gwajin layin dogon Jakarta-Bandung mai saurin tafiya. An fara aiki da tasoshin dakon kaya a layin dogo tsakanin kasar Sin da kasar Laos.

Kana an fara amfani da babban titin dake tsakanin Phnom Penh da tashar jiragen ruwa ta Sihanoukville a kasar Cambodiya. Lalle ayyukan raya ababen more rayuwar jama’a karkashin inuwar shawarar “ziri daya da hanya daya”, sun kyautata hadewar sassa daban daban a Asiya da yankin tekun Pasifik.

Kasar Sin za ta ci gaba da daukar hakikanin matakai don nuna yadda take aza harsashi a Asiya da yankin tekun Pasifik, da raya yankin da kuma kawo alheri ga yankin. (Tasallah Yuan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lauyoyin Arewa Sun Zargi EFCC Da Nuna Wariya Kan Wadanda Ake Zargi Da Badakalar Kudade

Next Post

Zamantakewar Aure Tsakanin Miji Da Mata: Wa Aka Fi Zalunta?

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

40 minutes ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

53 minutes ago
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

20 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

21 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

23 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

23 hours ago
Next Post
Zamantakewar Aure Tsakanin Miji Da Mata: Wa Aka Fi Zalunta?

Zamantakewar Aure Tsakanin Miji Da Mata: Wa Aka Fi Zalunta?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.