• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Jami’ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51

by Muhammad
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Mataimakin Shugaban Jami’ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin shugaban jami’ar jihar Kwara (KWASU), Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN), ya rasu.

Akanbi mai shekaru 51, ya rasu ne a ranar Lahadin da ta gabata a wani asibiti da ke jihar Legas.

  • ‘Yan Bindigar Da Suka Yi Garkuwa Da Malami Da Dansa A Kwara, Sun Bukaci Fansar Miliyan 100
  • EFCC Ta Kama ‘Yan Damfara 18 A Jihar Kwara 

Hukumar jami’ar ta tabbatar da mutuwar Akanbi a wata sanarwa da magatakardar jami’ar, Dokta Kikelomo Sally, ya sanyawa hannu.

Kafin a nada shi a matsayin mataimakin shugaban KWASU shekaru biyu da suka wuce, Akanbi malamin shari’a ne a Jami’ar Ilorin (UNILORIN).

“Cikin alhini muna mika wuya ga Allah, Hukumar Gudanarwar Jami’ar Jihar Kwara ta sanar da rasuwar Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN).

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana rashin Akanbi a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da kaduwa da mutuwar tasa.

“Mun mika wuya ga hukuncin Allah wanda yake bayarwa kuma yake karba. A kan wannan muke jimamin rasuwar mataimakin shugaban jami’ar da ya amsa kiran Allah a daren yau. Bawan Allah ne na gaskiya kuma mai kaskantar da kai, muna rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya ba shi Aljannar Firdausi.

“Farfesa a fannin shari’a kwararre ne wanda ya taka rawa wajen bude wani sabon babi na daukaka KWASU. Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa, kai tsaye zuwa ga KWASU da sauran malamai, da ’yan jihar Kwara da ma fadin kasar nan,” in ji gwamnan a wata sanarwa da babban mai yada labaransa ya sanya wa hannu, Rafiu Ajakaye.

A cikin sakon ta’aziyyar Sarkin Ilorin, Alh Ibrahim Sulu-Gambari, ya bayyana alhininsa game da rasuwar Akanbi.

Sulu-Gambari ya bayyana lamarin a matsayin abin ban tsoro, abin bantsoro da damuwa, yana mai jaddada cewa mutuwar Akanbi babban rashi ne ga al’ummar Masarautar Ilorin, Kwara da kuma Jama’a baki daya.

Sakon ta’aziyyar Sarkin na dauke da sa hannun mai magana da yawunsa, Malam Abdulazeez Arowona, ya ce: “Shi (Akanbi) ya kasance kwafin mahaifinsa kuma tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC), Marigayi Mai shari’a Mustapha Akanbi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwaraKwasuRasuwar Akanbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Ya Kamata A Dauki Batun Makamashi Na Kasashen Afirka Da Muhimmanci Don Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayin Duniya

Next Post

Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Related

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

2 weeks ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

3 weeks ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

4 weeks ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

1 month ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

2 months ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

2 months ago
Next Post
Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.