ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

by Muhammad
4 years ago
Wike

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, a daren Lahadi ya tarbi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar (NNPP), Rabi’u Kwankwaso, a Birnin Fatakwal, babban birnin jihar, gabanin kaddamar da titin Mgbutanwo da ke karamar hukumar Emohua a yau Litinin.

Wike ya gayyaci ‘yan siyasa daga jam’iyyun adawa zuwa bude ayyukansa daban-daban a Ribas, ya ce ya gayyaci ‘yan siyasa daga Jam’iyyun adawa don bude ayyuka a jiharsa domin su gani da idonsu su kuma shaida wa ’yan jam’iyyunsu.

  • 2023: Wike Zai Goyi Bayan Peter Obi Ya Yi Watsi Da Takarar Atiku
  • Rikicin PDP: Ina Farin Ciki Da Sulhun Da Rundunar Wike Ta Nemi A Yi – Atiku

Tsohon shugaban jam’iyyar (APC) na kasa, Adams Oshiomhole a ranar Larabar da ta gabata ya kaddamar da gadar sama ta 8 a jihar da ke kan titin Ada George, cikin karamar hukumar Obio-Akpor.

ADVERTISEMENT

Shi ma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya kaddamar da gadar sama ta 9 a babbar mahadar Ikoku a ranar Alhamis.

Hakazalika, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da makarantar koyon aikin lauya ta Nijeriya a Fatakwal ranar Juma’a.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Kusan kimanin watanni, Wike da wasu gwamnoni hudu na jam’iyyar PDP da aka fi sani da ‘Yan G5 suna neman shugaban Jam’iyyar, Iyorchia Ayu da ya yi murabus, suna masu cewa bai kamata ‘yan Arewa su zama shugaban jam’iyyar PDP na kasa ba kuma dan takarar shugaban kasa ya fito daga yankin ba.

Sai dai kuma, Ayu, dan asalin jihar Benue, ya dage kan cewa ba zai sauka ba har sai karshen wa’adinsa na shekaru hudu sun cika, ‘Yan G5 din sun gindaya sharadin sai ya yi murabus a matsayin wani sharadi na goyon bayan Atiku Abubakar, a zaben 2023.

Yayin da ba a ganin Wike da abokansa suna yi wa Atiku kamfen ba, ba a san ko za su goyi bayan Bola Tinubu na jam’iyyar APC ko Obi ba a takarar neman kujerar fadar Aso Rock wanda manazarta da masu lura da al’amura suka bayyana a matsayin tseren doki uku.

Wike
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Kwamandojin ‘Yan Ta’adda, Ba’a Usman, Alhaji Ari, Da Wasu Da Dama Sun Mika Wuya Ga Sojoji

Kwamandojin ‘Yan Ta’adda, Ba’a Usman, Alhaji Ari, Da Wasu Da Dama Sun Mika Wuya Ga Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.