• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

FILE - Pedestrians shop at a street market in Lagos, Nigeria, on Sept. 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba, File)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau na ga wannan labari: Charles Onunaiju, wani masanin ilimin huldar kasa da kasa na Najeriya, ya ce asusun tarayyar Amurka na ci gaba da kara kudin ruwa, matakin da ke iya haifar da mummunan tasiri ga kasashe masu tasowa.

Don neman shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki, asusun tarayyar Amurka ya kara kudin ruwa har sau 6, tun farkon shekarar 2022.

  • Sin: Gaskiya Ba Ta Buya, Kuma Adalci Yana Bayyana Kansa

Amma me ya sa matakin ya shafi sauran kasashe? Saboda wannan manufar za ta janyo dalar Amurka daga kasuwannin kasa da kasa, don su koma kasar Amurka. Hakan kuma zai sa a dinga canza kudaden sauran kasashe zuwa dalar Amurka, lamarin da zai haddasa faduwar darajar kudaden, da hauhawar farashin kayayyaki a wadannan kasashe, da karancin dalar Amurka, da jarin waje a kasuwanninsu, gami da raguwar adadin kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasashen waje.

Don tinkarar wannan mummunan tasiri, manyan bankunan sauran kasashe su ma sun daga kudin ruwa don neman kiyaye dalar Amurka a gida. Misali, babban bankin Najeriya ya riga ya daga kudin ruwa zuwa 16.5%. Sai dai manufar ba ta yi amfani sosai ba, ganin yadda darajar Naira na ci gaba da raguwa. A sa’i daya kuma, karuwar kudin ruwa na haifar da karin matsin lamba ga kamfanonin da suka ci bashi daga bankuna.

A cewar Charles Onunaiju, yanzu Nijeriya na fama da hauhawar farashin kayayyaki da matsalar karancin dalar Amurka a kasuwa, da faduwar darajar kudin kasar da dai sauransu, galibi saboda yadda take fuskantar matsin lamba daga wasu manufofin kasashen ketare. Kana Najeriya da sauran kasashe masu tasowa na fuskantar matsalolin raguwar guraben aikin yi, da karuwar bashin da ake ci. Ta wata manufarta kadai, kasar Amurka ta tura matsalolin hauhawar farashin kayayyaki, da koma bayan tattalin arziki, ga sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Matakan “kashin dankali” mai kama da wannan, da kasar Amurka ta yi wa sauran kasashe, sun yi yawa. Idan har mun dauki aminan kasar Amurka, wato kasashen Turai a matsayin misali. Ta hanyar fakewa da maganar daidaita yanayin da ake ciki a nahiyar Turai a fannin tsaro, kasar Amurka ta mai da kasashen Turai karkashin jagorancinta. Kana ta yi amfani da matsalar karancin makamashin da kasashen Turai suke fuskanta wajen sayar musu da iskar gas mai tsada matuka. Ban da wannan kuma, kasar Amurka ta ba da dimbin tallafi ga sana’ar kirkiro motoci masu amfani da lantarki ta kasar, don janyo masana’antun Turai zuwa gidanta. Ga shi, kasar ba ta kyautatawa aminanta, balle ma sauran kasashe.

A wannan zamanin da muke ciki, wata kasa kadai take samun dimbin tallafi daga kasar Amurka, wato kasar Ukraine. Amma dalilin da ya sa haka, shi ne Amurka na yin amfani da Ukraine wajen raunana kasar Rasha. An biya kudi, don sanya mutanen kasar Ukraine, maimakon na kasar Amurka zub da jini. Gaskiya Amurkawa suna da wayo.

Shafin yanar gizo ta Internet ta Modern Diplomacy, na Turai, ya ce kasar Amurka kasa ce dake son kwatar dukiyoyi daga sauran kasashe. Ko da yake wata babbar kasa ce, amma za ka yarda da manufarta ta “kashin dankali”?(Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mata Da Yara Akalla 721 Aka Yi Wa Fyade Cikin Watanni 9 A Kano

Next Post

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

14 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

15 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

17 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

2 days ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

2 days ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Dauki Karin Masu Share Tituna Don Tsaftace Muhalli

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.