• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

by Bello Hamza
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayani ya nuna cewa, matan tubabbun ‘yan ta’addan Boko Haram da na ‘yan kungiyar ISWAP da ke zaune a sansanin Hajj Camp da ke Maiduguri babban birnin Jihar Borno sun haifi jarirai 262 a cikin wata 4 kacal da suka gabata.

‘Yan ta’addan dai na rayuwa ne a cikin kananan gidajen da suka gina a cikin sansanin tare da mata da yaransu inda suke gudanar da rayuwa ba tare da wata mastala ba. Ana samun labarin haihuwa a kai kai a tsakanin iyalan tubabban ‘yan ta’addan.

  • Jirgin C919 Na Kasar Sin Ya Samu Amincewar Kara Kera Shi
  • CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022

Sansanin Hajj Camp na daya daga cikin sansanin hudu da gwamnati ta gina don killace ‘yan ta’addan da suka mika wuya ga dakarun Nijeriya a fagen fama.

Kididdigar ya nuna cewa, cikin jariran da aka haifa akwai mata 150 da maza 112. A watan Yuli na wannan shekarar an haifi yara 94 a sansanin yayin da aka haifi yara 98 a watan Agusta, an kuma haifi jarirai 60 a watan Satumba yayin da aka haifi jarirai 11 a watan Oktoba, kamar yadda kididdigar hukumar da ke kula da sansanin ta bayyana.

Mai kula da dakin shan maganin sansanin na Hajj Camp, Dakta Mohammed Sale ya sanar da haka a ziyarar da tawagar bincike suna kai masa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Da aka tambaye shi ko an taba samun mace-macen jarirai ko kuma matsalar da ta shafi haihuwa? Saioya bayyana cewa, ba su taba samun wata matsala ba, kuma duk wani aiki da ya fi karfinsu suna mika shi ne ga babban asibiti jihar mai suna’ Umoru Shehu Specialist Hospital’ ko kuma asibitin koyarswa na jami’ar Maiduguri.

Bayani ya nuna cewa,a daidai ranar 11 ga watan Nuwamba na shekarar 2022, mutanen da ke zaune a sansanin sun kai 14,804, Maza sun kai 5,200 kuma dukkan su mayaka ‘yan ta’adda ne, jami’an tsaro sun kashe ire-irensu da dama a yankin arewa maso gabas suma ‘yan ta’adda sun kashe al’umma da dama a yankin arewa maso gabas da suka hada da Borno, Yobe da Adamawa.

Daga cikin tubabbun ‘yan Boko Haram din da ke a sasanin na Hajj Camp, 3,427 na zaune ne da matansu yayin da 1,773 basa tare da matan su. Akwai matan aure 4,443 a sansanin. Wannan bayan wasu matan da ke zaune a sauran sansani uku da ke a wasu sassan jihar.

Bayani ya kuma nuna cewa akwai yara fiye da 5,170 a sansanin na Hajj Camp, maza 2,691 mata 2,479.

Mai bayar da shawara na musamman ga gwamnan Borno a kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdullahi Sabi Ishak (Mai Ritaya) ya bayyana cewa, fiye da tubbbabun mayakan 3,500 ne gwammnati ta mayar dasu a cikin al’umma, suna can sun cigaba da harkokin rayuwarsu.

Ita kuwa Kwamishinar Harkokin Mata ta Jihar Borno, Hajiya Zuwaira Gambo, ta bayyana cewa, gwamnati na samarwa tubabbun mayakan magungunan kula da lafiyar kwakwalwa da kuma tallafin bunkasa rayuwarsu, haka kumma ana samu tallafin daga gwamnatin tarayya da wasu kungiyoyi masu bayar da tallafi daga kasashen waje.

A nasa gudummawar, Shehun Borno Dakta Abubakar Umar Garbai ya nuna jin dadinsa ga kokarin jami’an tsaro a yankin, ya ce a halin yanzu babu wani yankin karammar hukuma da ke a hannun mayakan Boko Haram.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramHaihuwaJarirai
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Muradun CAN Da Na Dattawan Arewa A Sikeli

Next Post

Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

Related

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

2 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

4 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

4 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

5 hours ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

7 hours ago
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

8 hours ago
Next Post
Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.