ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

by Bello Hamza
4 years ago
Boko Haram

Bayani ya nuna cewa, matan tubabbun ‘yan ta’addan Boko Haram da na ‘yan kungiyar ISWAP da ke zaune a sansanin Hajj Camp da ke Maiduguri babban birnin Jihar Borno sun haifi jarirai 262 a cikin wata 4 kacal da suka gabata.

‘Yan ta’addan dai na rayuwa ne a cikin kananan gidajen da suka gina a cikin sansanin tare da mata da yaransu inda suke gudanar da rayuwa ba tare da wata mastala ba. Ana samun labarin haihuwa a kai kai a tsakanin iyalan tubabban ‘yan ta’addan.

  • Jirgin C919 Na Kasar Sin Ya Samu Amincewar Kara Kera Shi
  • CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022

Sansanin Hajj Camp na daya daga cikin sansanin hudu da gwamnati ta gina don killace ‘yan ta’addan da suka mika wuya ga dakarun Nijeriya a fagen fama.

ADVERTISEMENT

Kididdigar ya nuna cewa, cikin jariran da aka haifa akwai mata 150 da maza 112. A watan Yuli na wannan shekarar an haifi yara 94 a sansanin yayin da aka haifi yara 98 a watan Agusta, an kuma haifi jarirai 60 a watan Satumba yayin da aka haifi jarirai 11 a watan Oktoba, kamar yadda kididdigar hukumar da ke kula da sansanin ta bayyana.

Mai kula da dakin shan maganin sansanin na Hajj Camp, Dakta Mohammed Sale ya sanar da haka a ziyarar da tawagar bincike suna kai masa.

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

Da aka tambaye shi ko an taba samun mace-macen jarirai ko kuma matsalar da ta shafi haihuwa? Saioya bayyana cewa, ba su taba samun wata matsala ba, kuma duk wani aiki da ya fi karfinsu suna mika shi ne ga babban asibiti jihar mai suna’ Umoru Shehu Specialist Hospital’ ko kuma asibitin koyarswa na jami’ar Maiduguri.

Bayani ya nuna cewa,a daidai ranar 11 ga watan Nuwamba na shekarar 2022, mutanen da ke zaune a sansanin sun kai 14,804, Maza sun kai 5,200 kuma dukkan su mayaka ‘yan ta’adda ne, jami’an tsaro sun kashe ire-irensu da dama a yankin arewa maso gabas suma ‘yan ta’adda sun kashe al’umma da dama a yankin arewa maso gabas da suka hada da Borno, Yobe da Adamawa.

Daga cikin tubabbun ‘yan Boko Haram din da ke a sasanin na Hajj Camp, 3,427 na zaune ne da matansu yayin da 1,773 basa tare da matan su. Akwai matan aure 4,443 a sansanin. Wannan bayan wasu matan da ke zaune a sauran sansani uku da ke a wasu sassan jihar.

Bayani ya kuma nuna cewa akwai yara fiye da 5,170 a sansanin na Hajj Camp, maza 2,691 mata 2,479.

Mai bayar da shawara na musamman ga gwamnan Borno a kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdullahi Sabi Ishak (Mai Ritaya) ya bayyana cewa, fiye da tubbbabun mayakan 3,500 ne gwammnati ta mayar dasu a cikin al’umma, suna can sun cigaba da harkokin rayuwarsu.

Ita kuwa Kwamishinar Harkokin Mata ta Jihar Borno, Hajiya Zuwaira Gambo, ta bayyana cewa, gwamnati na samarwa tubabbun mayakan magungunan kula da lafiyar kwakwalwa da kuma tallafin bunkasa rayuwarsu, haka kumma ana samu tallafin daga gwamnatin tarayya da wasu kungiyoyi masu bayar da tallafi daga kasashen waje.

A nasa gudummawar, Shehun Borno Dakta Abubakar Umar Garbai ya nuna jin dadinsa ga kokarin jami’an tsaro a yankin, ya ce a halin yanzu babu wani yankin karammar hukuma da ke a hannun mayakan Boko Haram.

Boko Haram
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

MASU ALAKA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa
Manyan Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Next Post
Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.