ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Rasha Da Yukrain: Buhari Ya Koka Da Kwararowar Makamai Afirka

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
Buhari

A ranar Talata ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa a halin yanzu makaman da ake amfani da su a yakin da ake tafkawa a tsakanin kasar Rasha da Yukrain sun fara shigowa yakin tafkin tekun Chadi, inda daga na za su bazu zuwa sauran kasashen Afrika, wanda hakan zai cigaba da kara wutar mastalar tsaron da ake fuskanta a yankin.

Ita dai yankin kogin Chadi yana da dinbin albarkan tattalin arziki ya kuma hada yankunan Yammaci da Tsakiyar Afrika da suka hada da kasashen Cameroon, Chadi, Nijar da Nijeriya.

  • 2023: Muradun CAN Da Na Dattawan Arewa A Sikeli
  • Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

Shugabga Buhari ya yi wannan bayanin ne a yayin bude babba taron shugabannin kungiyar kasashen yakin tafkin kogin Chadi a karo na 16 da aka yi a babban dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja, shugaban kasa wanda kuma shi ne shugaban kungiyar, ya ce, yakin na Rasha da Yukrain ya kara haifar da bazuwa kananan makamai a sassan duniya wanda hakan kuma ya karfafa kirar bukatar a kara tabbatar da tsaro a iyakokin kasashen yankin don katse yiwuwar shigowar makamai daga wadannan yankin.

ADVERTISEMENT

Daga nan shugaban kasa Buhari ya kuma kara bayyana cewa, rikicin kasar Rasha da Yukrain da saura yankunan da ke fuskantar tashe-tashen hankula suka bunkasa harkokin ‘yan ta’addan Boko Haram a yankin Yammacin Afrika.

Ya ce, duk da kokarin da ake yi na rage karfin ‘yan Boko Haram, har yanzu kungiyar na nan na cigaba da ayyukanta na ta’addanci.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

“Ina farin cikin sanar da ku cewa, akan wannan shawarar muka karfafa ayyukan rundunar hadin gwiwa na MNJTF inda suka gudanar da aikinsu cikin nasara ta hanyar gabatar da rukunin aikin fafatawa har sau uku da aka sa wa suna kamar haka ’Ops‘YANCIN TAFKI (I&II) da ‘Ops Lake Sanity I’ da kuma ‘Ops Lake Sanity II’, za kuma a shirya mataki na gaba ne bayan tattara bayanai da darussan da aka cimma a shirye-shiryen mu na baya.

“Ina ma farin cikin sanar da ku cewa a yayin gabatar da farmakin ‘Ops Lake Sanity I’ an samu nasarar kashe mayakan Boko Haram da dama.

“ya za dole mu kwana da sanin cewa, duk wadanna nasarorin da kungiyar MNJTF ta samu a kan ‘yan ta’addan har yanzu akwai barazanar ‘yan ta’adda a wasu yankunanmu.

A nasa jawabin, babban sakataren hukumar LCBC, Ambasada Mamman Nuhu, ya sanar da cewa, Nijeriya ta biya kasonta na Dala 209,075,748 don tafiyar da rundunar hadin gwiwa ta MNJTF daga shekarar 2015 zuwa 2021.

Taron ya samu halartar shugabanni 6 na kasashen kungiyar in banda shugaban kasa Cameron, Paul Biya wanda ya samu wakilcin daya daga cikin ministocinsa.

Shugabannin kasashe da suka samu hakarta sun hada da Farfesa Faustine Archange TOUADERA, na Jamhoriyya Afrika ta Tsakiya; Mohamed BAZOUM, na kasa Nijar; Patrice TALLON, na jamhoriyyar Benin; Mahamat Idriss Deby ITNO, na kasar Chad da Mohamed AL-MENFI, na kasar Libya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Da Dumi-duminsa: 'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.