ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Rasha Da Yukrain: Buhari Ya Koka Da Kwararowar Makamai Afirka

by Bashir Bello, Abuja
4 years ago
Buhari

A ranar Talata ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa a halin yanzu makaman da ake amfani da su a yakin da ake tafkawa a tsakanin kasar Rasha da Yukrain sun fara shigowa yakin tafkin tekun Chadi, inda daga na za su bazu zuwa sauran kasashen Afrika, wanda hakan zai cigaba da kara wutar mastalar tsaron da ake fuskanta a yankin.

Ita dai yankin kogin Chadi yana da dinbin albarkan tattalin arziki ya kuma hada yankunan Yammaci da Tsakiyar Afrika da suka hada da kasashen Cameroon, Chadi, Nijar da Nijeriya.

  • 2023: Muradun CAN Da Na Dattawan Arewa A Sikeli
  • Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

Shugabga Buhari ya yi wannan bayanin ne a yayin bude babba taron shugabannin kungiyar kasashen yakin tafkin kogin Chadi a karo na 16 da aka yi a babban dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja, shugaban kasa wanda kuma shi ne shugaban kungiyar, ya ce, yakin na Rasha da Yukrain ya kara haifar da bazuwa kananan makamai a sassan duniya wanda hakan kuma ya karfafa kirar bukatar a kara tabbatar da tsaro a iyakokin kasashen yankin don katse yiwuwar shigowar makamai daga wadannan yankin.

ADVERTISEMENT

Daga nan shugaban kasa Buhari ya kuma kara bayyana cewa, rikicin kasar Rasha da Yukrain da saura yankunan da ke fuskantar tashe-tashen hankula suka bunkasa harkokin ‘yan ta’addan Boko Haram a yankin Yammacin Afrika.

Ya ce, duk da kokarin da ake yi na rage karfin ‘yan Boko Haram, har yanzu kungiyar na nan na cigaba da ayyukanta na ta’addanci.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“Ina farin cikin sanar da ku cewa, akan wannan shawarar muka karfafa ayyukan rundunar hadin gwiwa na MNJTF inda suka gudanar da aikinsu cikin nasara ta hanyar gabatar da rukunin aikin fafatawa har sau uku da aka sa wa suna kamar haka ’Ops‘YANCIN TAFKI (I&II) da ‘Ops Lake Sanity I’ da kuma ‘Ops Lake Sanity II’, za kuma a shirya mataki na gaba ne bayan tattara bayanai da darussan da aka cimma a shirye-shiryen mu na baya.

“Ina ma farin cikin sanar da ku cewa a yayin gabatar da farmakin ‘Ops Lake Sanity I’ an samu nasarar kashe mayakan Boko Haram da dama.

“ya za dole mu kwana da sanin cewa, duk wadanna nasarorin da kungiyar MNJTF ta samu a kan ‘yan ta’addan har yanzu akwai barazanar ‘yan ta’adda a wasu yankunanmu.

A nasa jawabin, babban sakataren hukumar LCBC, Ambasada Mamman Nuhu, ya sanar da cewa, Nijeriya ta biya kasonta na Dala 209,075,748 don tafiyar da rundunar hadin gwiwa ta MNJTF daga shekarar 2015 zuwa 2021.

Taron ya samu halartar shugabanni 6 na kasashen kungiyar in banda shugaban kasa Cameron, Paul Biya wanda ya samu wakilcin daya daga cikin ministocinsa.

Shugabannin kasashe da suka samu hakarta sun hada da Farfesa Faustine Archange TOUADERA, na Jamhoriyya Afrika ta Tsakiya; Mohamed BAZOUM, na kasa Nijar; Patrice TALLON, na jamhoriyyar Benin; Mahamat Idriss Deby ITNO, na kasar Chad da Mohamed AL-MENFI, na kasar Libya.

Buhari
Bashir Bello, Abuja
+ postsBio
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    APC Ce Za Ta Yi Nasarar Samar Da Shugabanci A Majalisa – Hon. Wase
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Da Dumi-duminsa: 'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.