• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sahihanci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sahihanci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, ko kuna son cin Avacado? Kun san a nan kasar Sin ba a noma wannan nau’in ‘ya’yan marmari, saboda haka kusan ba wanda ya san shi kafin shekaru fiye da 10 da suka wuce.

Na tuna lokacin da na sayi Avacado a karon farko, ban san ya kamata a bari ya yi laushi ba kafin a ci shi. Sai na ci shi nan take bayan da na same shi, yayin da yake da tauri. Don haka ra’ayin da na samu game da Avacado a lokacin shi ne, wani nau’in ‘ya’yan marmari ne mai tsada, kuma maras dadi.

  • An Gudanar Da Dandalin Matasan Sin Da Afirka Kan Ayyukan Sa Kai

Tabbas daga bisani na san hanya mafi dacewa da ya kamata a bi wajen dandana Avacado. Kana saboda Sinawa sun kara fahimtar amfaninsa a fannin gina jiki, hakan ya sa ana shigo da karin Avacado cikin kasar Sin. Misali, a shekarar 2010, an shigo da Avacado ton 2 ne kacal cikin kasuwannin kasar Sin, amma zuwa shekarar 2018, wannan adadi ya karu zuwa ton 43,860, inda darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 133.

Ban da wannan kuma, tun daga shekarar bana, kasar Sin ta fara shigo da Avavado daga wasu kasasahen Afirka, irinsu Kenya da Tanzania.

Hakan na daga cikin matakan da aka dauka na cika alkawarin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi a wani taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a bara, wato “Ba da sauki ga shigowar amfanin gonan Afirka cikin kasuwar kasar Sin, kana da kokarin shigo da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 30 daga kasashen Afirka, cikin shekaru 3 dake tafe.”
Me ya sa kasar Sin ke neman shigo da karin kayayyaki daga nahiyar Afirka? Dalili shi ne, kasar Sin na neman daidaita cinikayyar da ake yi tsakaninta da kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Bayanan da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta gabatar sun nuna cewa, ana samun daidaito tsakanin bangarorin Sin da Afirka ta fuskar ciniki.

Sai dai idan an tantance bayanai game da daidaikun kasa dake nahiyar Afirka, za a ga wasu kasashe na fitar da dimbin kayayyaki zuwa kasar Sin, yayin da wasu ba su samun damar fitar da kayayyakinsu sosai. Saboda haka, don raba moriya ga wadannan kasashe, kasar Sin ta dauki matakin shigo da karin kayayyakinsu.

Matakan da gwamnatin kasar Sin ta dauka a shekarun nan, sun hada da gudanar da tarukan baje kolin kayayyakin Afirka a kasar Sin, da kafa cibiyoyin nuna kayayyakin Afirka a wasu biranen kasar, da shirya bukukuwan tallace-tallacen kayayyakin Afirka a dandalin sayar da kaya ta kafar yanar gizo ta Internet, da samar da rance ga wasu kamfanonin kasar Sin domin su shigo da karin kayayyaki daga kasashen Afirka, da dai sauransu.

Kana sabbin matakan da kasar Sin ta dauka a bana, sun hada da fara shigo da Avacado daga kasashen Afirka, da yafe wa karin wasu kasashe mafi rashin karfin tattalin arziki harajin da ake karba bisa kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasar Sin, wadannan kasashe sun hada da Benin, da Burkina Faso, da Guinea Bissau, da Lesotho, da Malawi, da Sau Tome da Principe, da Tanzania, da Uganda, gami da Zambia.

Wadannan matakai sun nuna yadda kasar Sin take da sahihanci, yayin da take hadin gwiwa tare da kasashen Afirka. Idan ana son kulla huldar hadin kai mai dorewa, dole ne a kulla huldar cin gajiyar juna. Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da hakan? Amsa ita ce ta yin mu’ammala cikin daidaito, da daidaita matakai akai akai, ta yadda za a iya tabbatar da daidaituwar moriyar bangarori daban daban, da sanya kowa ya gamsu.

Wannan ma dalili ne da ya sa kasashen Afirka, ba sa amincewa da wasu maganganu marasa kyau da wasu kasashe suka fada, game da huldar hadin gwiwar Afirka da Sin.

Kasashen Afirka sun ga sahihancin da kasar Sin ta nuna, kuma sun san duk wata matsalar da aka samu, yayin da ake hadin kai da kasar Sin, za a iya warware ta ta hanyar mu’ammala, da daidaita manufofi. Saboda haka, ba su damuwa game da huldar hadin kai da suka kulla tare da kasar ta Sin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cafke Wasu Ma’aurata Kan Zargin Hada Baki Wajen Bizne Jaririyarsu Da Ranta A Jigawa

Next Post

2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

Related

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 
Daga Birnin Sin

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

5 seconds ago
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

20 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

21 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

22 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

24 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

1 day ago
Next Post
2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

2023: Buhari Ya Hori Jami'an Tsaro Su Zama 'Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

June 5, 2025
Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.