ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sahihanci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

by CMG Hausa
4 years ago
Afirka

Abokaina, ko kuna son cin Avacado? Kun san a nan kasar Sin ba a noma wannan nau’in ‘ya’yan marmari, saboda haka kusan ba wanda ya san shi kafin shekaru fiye da 10 da suka wuce.

Na tuna lokacin da na sayi Avacado a karon farko, ban san ya kamata a bari ya yi laushi ba kafin a ci shi. Sai na ci shi nan take bayan da na same shi, yayin da yake da tauri. Don haka ra’ayin da na samu game da Avacado a lokacin shi ne, wani nau’in ‘ya’yan marmari ne mai tsada, kuma maras dadi.

  • An Gudanar Da Dandalin Matasan Sin Da Afirka Kan Ayyukan Sa Kai

Tabbas daga bisani na san hanya mafi dacewa da ya kamata a bi wajen dandana Avacado. Kana saboda Sinawa sun kara fahimtar amfaninsa a fannin gina jiki, hakan ya sa ana shigo da karin Avacado cikin kasar Sin. Misali, a shekarar 2010, an shigo da Avacado ton 2 ne kacal cikin kasuwannin kasar Sin, amma zuwa shekarar 2018, wannan adadi ya karu zuwa ton 43,860, inda darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 133.

ADVERTISEMENT

Ban da wannan kuma, tun daga shekarar bana, kasar Sin ta fara shigo da Avavado daga wasu kasasahen Afirka, irinsu Kenya da Tanzania.

Hakan na daga cikin matakan da aka dauka na cika alkawarin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi a wani taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a bara, wato “Ba da sauki ga shigowar amfanin gonan Afirka cikin kasuwar kasar Sin, kana da kokarin shigo da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 30 daga kasashen Afirka, cikin shekaru 3 dake tafe.”
Me ya sa kasar Sin ke neman shigo da karin kayayyaki daga nahiyar Afirka? Dalili shi ne, kasar Sin na neman daidaita cinikayyar da ake yi tsakaninta da kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Bayanan da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta gabatar sun nuna cewa, ana samun daidaito tsakanin bangarorin Sin da Afirka ta fuskar ciniki.

Sai dai idan an tantance bayanai game da daidaikun kasa dake nahiyar Afirka, za a ga wasu kasashe na fitar da dimbin kayayyaki zuwa kasar Sin, yayin da wasu ba su samun damar fitar da kayayyakinsu sosai. Saboda haka, don raba moriya ga wadannan kasashe, kasar Sin ta dauki matakin shigo da karin kayayyakinsu.

Matakan da gwamnatin kasar Sin ta dauka a shekarun nan, sun hada da gudanar da tarukan baje kolin kayayyakin Afirka a kasar Sin, da kafa cibiyoyin nuna kayayyakin Afirka a wasu biranen kasar, da shirya bukukuwan tallace-tallacen kayayyakin Afirka a dandalin sayar da kaya ta kafar yanar gizo ta Internet, da samar da rance ga wasu kamfanonin kasar Sin domin su shigo da karin kayayyaki daga kasashen Afirka, da dai sauransu.

Kana sabbin matakan da kasar Sin ta dauka a bana, sun hada da fara shigo da Avacado daga kasashen Afirka, da yafe wa karin wasu kasashe mafi rashin karfin tattalin arziki harajin da ake karba bisa kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasar Sin, wadannan kasashe sun hada da Benin, da Burkina Faso, da Guinea Bissau, da Lesotho, da Malawi, da Sau Tome da Principe, da Tanzania, da Uganda, gami da Zambia.

Wadannan matakai sun nuna yadda kasar Sin take da sahihanci, yayin da take hadin gwiwa tare da kasashen Afirka. Idan ana son kulla huldar hadin kai mai dorewa, dole ne a kulla huldar cin gajiyar juna. Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da hakan? Amsa ita ce ta yin mu’ammala cikin daidaito, da daidaita matakai akai akai, ta yadda za a iya tabbatar da daidaituwar moriyar bangarori daban daban, da sanya kowa ya gamsu.

Wannan ma dalili ne da ya sa kasashen Afirka, ba sa amincewa da wasu maganganu marasa kyau da wasu kasashe suka fada, game da huldar hadin gwiwar Afirka da Sin.

Kasashen Afirka sun ga sahihancin da kasar Sin ta nuna, kuma sun san duk wata matsalar da aka samu, yayin da ake hadin kai da kasar Sin, za a iya warware ta ta hanyar mu’ammala, da daidaita manufofi. Saboda haka, ba su damuwa game da huldar hadin kai da suka kulla tare da kasar ta Sin. (Bello Wang)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

2023: Buhari Ya Hori Jami'an Tsaro Su Zama 'Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.