• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Dai Mu Gani

by CMG Hausa
3 years ago

A yayin da kasar Amurka ta shirya wani babban taron tattaunawa da shugabannin Afirka a birnin Washignton D.C, sai ga shi wani sabon rahoton bincike da Gallup ya gudanar na nuna cewa, farin jinin fadar White House da majalisar dokokin kasar na ci gaba da raguwa.

Koda yake ba dukkan shugabannin nahiyar aka gayyata ba, bisa wasu dalilai da Amurkar da barwa kanta sani. Masu iya magana dai na cewa, idan ka so uwa to ka so ‘ya’yanta.

  • Kasar Sin Ta Shigar Da Kara A WTO Kan Matakin Amurka Na Hana Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasashen Waje

A cewar rahoton, kaso 40 cikin 100 na Amurkawa da aka tambaya ne suka nuna amincewa da kimar shugaban Amurka joe Biden, yayin da kashi 55 cikin 100 suka nuna amincewa da yadda yake tafiyar da aikinsa. Tambayar ita ce, wai me ya sa shugabannin Amurka suka gayyaci shugabannin wasu kasashen Afirka a cikin hali da kimarsu ke raguwa? Ruwa dai aka ce ba ya tsami banza.

Bugu da kari, kuri’ar nuna rashin amincewa da Biden ta ci gaba da karuwa, tun watan Satumba shekarar 2021, bayan da sojojin Amurka suka janye daga Afghanistan.

A halin da ake ciki kuma yanzu, yadda Amurkawa ke nuna rashin amincewa da majalisar dokokin kasar, abin babu dadin ji ko kadan, inda kashi 73 cikin 100 na baligai Amukawa ke nuna rashin amincewa da kimar majalisar. Ko da yake tsuntsun da ya jawo ruwa…

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

An wallafa sakamakon wannan binciken kuri’ar jin ra’ayin jama’a ne daga ranar 9 ga watan Nuwamba zuwa 2 ga watan Disamba, wanda Gallup ya gudanar, bayan zaben tsakiyar wa’adi na ranar 8 ga watan Nuwamban shekarar 2022.

Sanin kowa ne cewa, duk wani tallafi da Amurka za ta baiwa wata kasa, sai ya samu amincewar majalisun kasar, ga shi kuma sharhin da Gallup ya rubuta na bayyana cewa, majalisar dokokin Amurka za ta fuskanci rabuwar kawuna a cikin shekaru biyu dake tafe, bayan da ‘yan jam’iyyar Republican suka kwace ikon majalisar, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat ke da rinjaye a majalisar dattawa. Don haka, ta yaya Amurka za ta iya agazawa kasashen na Afirka cikin wannan hali na rudani? Koma dai mene ne, yanzu ya rage wa shugabannin Afirka da aka gayyata, su karkade kunnuwansu, don jin sabuwar tatsuniyar da za a fada musu. Dabara kuma ta rage ga mai shiga rijiya. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi – Messi

Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi - Messi

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.