• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Dai Mu Gani

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
A Yi Dai Mu Gani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da kasar Amurka ta shirya wani babban taron tattaunawa da shugabannin Afirka a birnin Washignton D.C, sai ga shi wani sabon rahoton bincike da Gallup ya gudanar na nuna cewa, farin jinin fadar White House da majalisar dokokin kasar na ci gaba da raguwa.

Koda yake ba dukkan shugabannin nahiyar aka gayyata ba, bisa wasu dalilai da Amurkar da barwa kanta sani. Masu iya magana dai na cewa, idan ka so uwa to ka so ‘ya’yanta.

  • Kasar Sin Ta Shigar Da Kara A WTO Kan Matakin Amurka Na Hana Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasashen Waje

A cewar rahoton, kaso 40 cikin 100 na Amurkawa da aka tambaya ne suka nuna amincewa da kimar shugaban Amurka joe Biden, yayin da kashi 55 cikin 100 suka nuna amincewa da yadda yake tafiyar da aikinsa. Tambayar ita ce, wai me ya sa shugabannin Amurka suka gayyaci shugabannin wasu kasashen Afirka a cikin hali da kimarsu ke raguwa? Ruwa dai aka ce ba ya tsami banza.

Bugu da kari, kuri’ar nuna rashin amincewa da Biden ta ci gaba da karuwa, tun watan Satumba shekarar 2021, bayan da sojojin Amurka suka janye daga Afghanistan.

A halin da ake ciki kuma yanzu, yadda Amurkawa ke nuna rashin amincewa da majalisar dokokin kasar, abin babu dadin ji ko kadan, inda kashi 73 cikin 100 na baligai Amukawa ke nuna rashin amincewa da kimar majalisar. Ko da yake tsuntsun da ya jawo ruwa…

Labarai Masu Nasaba

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

An wallafa sakamakon wannan binciken kuri’ar jin ra’ayin jama’a ne daga ranar 9 ga watan Nuwamba zuwa 2 ga watan Disamba, wanda Gallup ya gudanar, bayan zaben tsakiyar wa’adi na ranar 8 ga watan Nuwamban shekarar 2022.

Sanin kowa ne cewa, duk wani tallafi da Amurka za ta baiwa wata kasa, sai ya samu amincewar majalisun kasar, ga shi kuma sharhin da Gallup ya rubuta na bayyana cewa, majalisar dokokin Amurka za ta fuskanci rabuwar kawuna a cikin shekaru biyu dake tafe, bayan da ‘yan jam’iyyar Republican suka kwace ikon majalisar, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat ke da rinjaye a majalisar dattawa. Don haka, ta yaya Amurka za ta iya agazawa kasashen na Afirka cikin wannan hali na rudani? Koma dai mene ne, yanzu ya rage wa shugabannin Afirka da aka gayyata, su karkade kunnuwansu, don jin sabuwar tatsuniyar da za a fada musu. Dabara kuma ta rage ga mai shiga rijiya. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin PDP A Ribas: Atiku Muke Wa Biyayya Ba Wike Ba

Next Post

Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi – Messi

Related

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

10 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

11 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

12 hours ago
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

13 hours ago
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

14 hours ago
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

16 hours ago
Next Post
Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi – Messi

Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi - Messi

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.