ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Dai Mu Gani

by CMG Hausa
3 years ago

A yayin da kasar Amurka ta shirya wani babban taron tattaunawa da shugabannin Afirka a birnin Washignton D.C, sai ga shi wani sabon rahoton bincike da Gallup ya gudanar na nuna cewa, farin jinin fadar White House da majalisar dokokin kasar na ci gaba da raguwa.

Koda yake ba dukkan shugabannin nahiyar aka gayyata ba, bisa wasu dalilai da Amurkar da barwa kanta sani. Masu iya magana dai na cewa, idan ka so uwa to ka so ‘ya’yanta.

  • Kasar Sin Ta Shigar Da Kara A WTO Kan Matakin Amurka Na Hana Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasashen Waje

A cewar rahoton, kaso 40 cikin 100 na Amurkawa da aka tambaya ne suka nuna amincewa da kimar shugaban Amurka joe Biden, yayin da kashi 55 cikin 100 suka nuna amincewa da yadda yake tafiyar da aikinsa. Tambayar ita ce, wai me ya sa shugabannin Amurka suka gayyaci shugabannin wasu kasashen Afirka a cikin hali da kimarsu ke raguwa? Ruwa dai aka ce ba ya tsami banza.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, kuri’ar nuna rashin amincewa da Biden ta ci gaba da karuwa, tun watan Satumba shekarar 2021, bayan da sojojin Amurka suka janye daga Afghanistan.

A halin da ake ciki kuma yanzu, yadda Amurkawa ke nuna rashin amincewa da majalisar dokokin kasar, abin babu dadin ji ko kadan, inda kashi 73 cikin 100 na baligai Amukawa ke nuna rashin amincewa da kimar majalisar. Ko da yake tsuntsun da ya jawo ruwa…

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

An wallafa sakamakon wannan binciken kuri’ar jin ra’ayin jama’a ne daga ranar 9 ga watan Nuwamba zuwa 2 ga watan Disamba, wanda Gallup ya gudanar, bayan zaben tsakiyar wa’adi na ranar 8 ga watan Nuwamban shekarar 2022.

Sanin kowa ne cewa, duk wani tallafi da Amurka za ta baiwa wata kasa, sai ya samu amincewar majalisun kasar, ga shi kuma sharhin da Gallup ya rubuta na bayyana cewa, majalisar dokokin Amurka za ta fuskanci rabuwar kawuna a cikin shekaru biyu dake tafe, bayan da ‘yan jam’iyyar Republican suka kwace ikon majalisar, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat ke da rinjaye a majalisar dattawa. Don haka, ta yaya Amurka za ta iya agazawa kasashen na Afirka cikin wannan hali na rudani? Koma dai mene ne, yanzu ya rage wa shugabannin Afirka da aka gayyata, su karkade kunnuwansu, don jin sabuwar tatsuniyar da za a fada musu. Dabara kuma ta rage ga mai shiga rijiya. (Ibrahim Yaya)

CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi – Messi

Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi - Messi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.