• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Barazanar Jami’an Tsaro Ana Ci Gaba Da Kone-konen Ofisoshin INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Dakile Wani Hari A Ofishin INEC Dake Imo, Sun Kashe Maharan 3.
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ke Owerri Babban Birnin Jihar Imo.

Harin ya yi sanadiyyar lalacewar wani bangaren ofishin bayan da nakiya ta fashe.
Kakakin rundunar ‘yansandar Jihar Imo, Mike Abbatam, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai ya bayyana cewa an samu nasarar kashe maharan guda uku tare da gano bama-bamai guda biyu.

  • Ba Za Mu Bari A Ci Gaba Da Kai Hare-hare Ga Ofisoshin INEC Ba, Cewar Sufeton ‘Yansanda

Wannan lamari ya faru ne cikin kwanaki takwas bayan kai farmaki a ofishin INEC da ke karamar hukumar Orlu a cikin jihar.
Wadanda ake zargin ‘yan daba ne sun kai irin wannan farmakin a ofisoshin INEC da ke jihohin Ebonyi da Osun da kuma Ogun a makonni hudun da suka gabata, lamarin da ya fara saka wa mutane shakku kan yuwuwar gudanar da zaben 2023.

Farmakin na Owerri ya gudana ne da misalin karfe uku na dare, inda jami’an tsaro suka samu nasarar harbe uku ciki har da kwamandansu har lahira. An dai samu nasarar kwato bindigogin kirar AK47 da wasu masu sarrafa kansu da motoci takwas daga hannun maharan.

Wata majiya ta ce, “A safiyar Lininin ce wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin INEC da ke Owerri a Jihar Imo, amma tawagar jami’an tsaro sun samu nasarar bude musu wuta tare da halaka uku ciki har da kwamandarsu.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

“An samu nasarar kwato motoci bakwai ciki har da bindigogin AK47 da masu sarrafa kansu. Mafi yawancin ‘yan bindigan sun gudu da raunikan harbi. Amma sai dai ‘yan daban sun kone motar ‘yansanda guda daya.”
Sai dai shi kuma Abbattam ya ce bindigogi kirar AK47 guda uku da motoci aka samu nasarar kwacewa.

Ya ce, “Mun kashe guda uku daga cikin maharan tare da kwato bindigogi kirar AK47 da masu sarrafa kansu muka samu nasarar kwatowa daga hannun maharan. Haka kuma mun kwato abubuwan fashewa guda biyu da motoci uku.”

An dai bayyana cewa an jibge jami’an tsaro a wasu yankuna da ke Owerri sakamakon wannan lamari.

Sakamakon kone-konen ofisoshin INEC a wasu sassan kasar nan, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaron kasa (NSA), Majo Janar Babagana Monguno (rtd) da babban sufetan ‘yansanda na kasa, (IGP) Usman Baba Akali sun yi barazanar daukan mataki.

Dukkansu sun karanto laifukan da ke tattare da kone ofisoshin INEC, inda suka bayyana cewa an bai wa jamian tsaro umurnin kalubalantar duk wani mutum ko kungiya da ke kokarin kawo tsaiko kan zaben 2023.

Babban sufetan ‘yansanda ya bayyana cewa tuni ya umurci kwamishinonin ‘yansanda su samar da tsaro a dukkan ofisoshin INEC da ke jihohinsu.

A cewarsa, wannan aiki na wasu gurbatattun ‘yan siyasa ne da ke barazana ga zaben 2023.

Duk da wadannan zafafan hare-hare da ake kone-konen ofisoshin INEC, hukumar ta bayyana cewa ko kadan wannan ba zai iya hana gudanar da zaben 2023 ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

3 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

6 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

8 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

11 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

13 hours ago
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.