ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Barazanar Jami’an Tsaro Ana Ci Gaba Da Kone-konen Ofisoshin INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
INEC

Da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ke Owerri Babban Birnin Jihar Imo.

Harin ya yi sanadiyyar lalacewar wani bangaren ofishin bayan da nakiya ta fashe.
Kakakin rundunar ‘yansandar Jihar Imo, Mike Abbatam, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai ya bayyana cewa an samu nasarar kashe maharan guda uku tare da gano bama-bamai guda biyu.

  • Ba Za Mu Bari A Ci Gaba Da Kai Hare-hare Ga Ofisoshin INEC Ba, Cewar Sufeton ‘Yansanda

Wannan lamari ya faru ne cikin kwanaki takwas bayan kai farmaki a ofishin INEC da ke karamar hukumar Orlu a cikin jihar.
Wadanda ake zargin ‘yan daba ne sun kai irin wannan farmakin a ofisoshin INEC da ke jihohin Ebonyi da Osun da kuma Ogun a makonni hudun da suka gabata, lamarin da ya fara saka wa mutane shakku kan yuwuwar gudanar da zaben 2023.

ADVERTISEMENT

Farmakin na Owerri ya gudana ne da misalin karfe uku na dare, inda jami’an tsaro suka samu nasarar harbe uku ciki har da kwamandansu har lahira. An dai samu nasarar kwato bindigogin kirar AK47 da wasu masu sarrafa kansu da motoci takwas daga hannun maharan.

Wata majiya ta ce, “A safiyar Lininin ce wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin INEC da ke Owerri a Jihar Imo, amma tawagar jami’an tsaro sun samu nasarar bude musu wuta tare da halaka uku ciki har da kwamandarsu.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

“An samu nasarar kwato motoci bakwai ciki har da bindigogin AK47 da masu sarrafa kansu. Mafi yawancin ‘yan bindigan sun gudu da raunikan harbi. Amma sai dai ‘yan daban sun kone motar ‘yansanda guda daya.”
Sai dai shi kuma Abbattam ya ce bindigogi kirar AK47 guda uku da motoci aka samu nasarar kwacewa.

Ya ce, “Mun kashe guda uku daga cikin maharan tare da kwato bindigogi kirar AK47 da masu sarrafa kansu muka samu nasarar kwatowa daga hannun maharan. Haka kuma mun kwato abubuwan fashewa guda biyu da motoci uku.”

An dai bayyana cewa an jibge jami’an tsaro a wasu yankuna da ke Owerri sakamakon wannan lamari.

Sakamakon kone-konen ofisoshin INEC a wasu sassan kasar nan, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaron kasa (NSA), Majo Janar Babagana Monguno (rtd) da babban sufetan ‘yansanda na kasa, (IGP) Usman Baba Akali sun yi barazanar daukan mataki.

Dukkansu sun karanto laifukan da ke tattare da kone ofisoshin INEC, inda suka bayyana cewa an bai wa jamian tsaro umurnin kalubalantar duk wani mutum ko kungiya da ke kokarin kawo tsaiko kan zaben 2023.

Babban sufetan ‘yansanda ya bayyana cewa tuni ya umurci kwamishinonin ‘yansanda su samar da tsaro a dukkan ofisoshin INEC da ke jihohinsu.

A cewarsa, wannan aiki na wasu gurbatattun ‘yan siyasa ne da ke barazana ga zaben 2023.

Duk da wadannan zafafan hare-hare da ake kone-konen ofisoshin INEC, hukumar ta bayyana cewa ko kadan wannan ba zai iya hana gudanar da zaben 2023 ba.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.