• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aisha Buhari Za Ta Jagoranci Matan Gwamnoni A Fagen Yaki Da Cin Zarafin Mata

by Bello Hamza
3 years ago
in Labarai
0
Aisha Buhari Za Ta Jagoranci Matan Gwamnoni A Fagen Yaki Da Cin Zarafin Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari ta bayyana cewa, za a iya kawo karshen cin zarafin da ake yi wa mata da kananan yara a sassan kasar nan duk kuwa da yadda ake samun karuwar lamarin a ‘yan shekarun nan.

Aisha Buhari ta sanar da haka ne taron kungiyar matan gwamnonin Nijeriya karo na 3 a garin Abuja kwanakin baya, taron mai taken, “Fadakar da al’umma a kan dokar ta-baci a kan cin zarafin mata’.

  • Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

Ta kuma bukkaci kungiyar ta tabbatar da dorewar gangamin musamman ganin a halin yanzu an samu nasarar zartar da dokar kariya ga mata da kananan yara a jihohi 34 na tarrayar Nijeriya.

Uwargidan Shugaban kasar wadda ta samu wakilcin mataimakiyarta ta musamman a kan harkokin mata, Rukayyatu Abdulkareem Gurin, ta kara da cewa, lamarin cinzarafin mata na daya daga cikin abubuwan da aka tattauna a taron kwanaki 16 da aka yi inda waklilai daga kasashen duniya suka samu halarta, musamman ganin mastala ce da ake fama da ita a sassan duniya.

Ta yaba wa matan gwamnonin a kan yadda suka hada kai don ganin an samar da yanayi na kare mata da kananan yara daga cutarwa ta kowacce fuska.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Ta ce, “Hanyar samar da daidato da hanyoyin samun aiki ga mata na da matukar muhimmanci, Nijeriya ta yi gaggarumar nasara a wannan fannin, musamman in aka lura da yadda aka zartar da dokar haramta cin zarafin mata ‘ Biolence Against Persons Prohibition (BAPP)’ a wasu jihohi 34 na tarrayar kasar nan.

Ta kuma kara da cewa, kungiyar matan gwamnonin sun kudurin aniyar aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki doin ganin an rage yadda ake cin zarafin mata da kananan yara a kasar nan.

“Yakamata mu kuduri aniyar tabbatar da ganin kowacce mace ko yarinya ta samu ‘yancin rayuwa tare da cikakken kariya daga dukkan abin da zai iya cutar da ita,” in ji ta.
Ana shi jawabin, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya, kuma Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal, ya tabbatar wa da mata cewa, gwamnoni za su cigaba da bayar da gudummawar da ta kamata don ganin an kawo karshen cin zarafin mata a Nijeriya.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, saura jihohi 2 da basu sanya hannu a kan dokar kariya ga mata ba za su sa hannu nan ba da dadewa ba, ya kuma yaba wa matan gwamnonin a kan wannan kokarin, da yaba masu a kan yadda suka samar da yanayin shirin zai cigaba koda a bayansu ne.

Tunda farko, shugabar kungiyar na matan gwamnonin Nijeriya kuma uwargidan Gwamnan Jihar Sakkwato, Hajiya Mariya Aminu Tambuwal, ta ce, cikin makasudin kafa kungiyar sun hada da tattara masu ruwa da tsaki don ganin an fuskanci matsalar cin zarafin mata a Nijeriya.

Ita a nata jawabin, Ministar Harkokin Mata, Pauline Tallen, ta yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai a kan dokoki masu tsauri ga masu cin zarafin mata a jihar, a dokar wanda aka sanya wa hannu a watan Satumba 2021, an tanadi yin dandake ga wadanda aka samu da cin zarafin mata.

Dokar da aka yi wa kwaskwarima ta tanadi duk wani magidanci da aka kama ya yi wa yarinya ko yaro da shekarunsa suke kasa da 14 fyade a yi masa dandaka yayin da macen da aka kama ta yi wa ‘yan yara fyade ita ma za a cire mata mahaifa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Daba Sun Tarwatsa Taron APC, Sun Yi Awon Gaba Da Shugaban Matasa A Delta

Next Post

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Related

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

29 minutes ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

2 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

6 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

7 hours ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

9 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

10 hours ago
Next Post
Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.