ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aisha Buhari Za Ta Jagoranci Matan Gwamnoni A Fagen Yaki Da Cin Zarafin Mata

by Bello Hamza
3 years ago
Aisha Buhari

Uwargidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari ta bayyana cewa, za a iya kawo karshen cin zarafin da ake yi wa mata da kananan yara a sassan kasar nan duk kuwa da yadda ake samun karuwar lamarin a ‘yan shekarun nan.

Aisha Buhari ta sanar da haka ne taron kungiyar matan gwamnonin Nijeriya karo na 3 a garin Abuja kwanakin baya, taron mai taken, “Fadakar da al’umma a kan dokar ta-baci a kan cin zarafin mata’.

  • Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

Ta kuma bukkaci kungiyar ta tabbatar da dorewar gangamin musamman ganin a halin yanzu an samu nasarar zartar da dokar kariya ga mata da kananan yara a jihohi 34 na tarrayar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Uwargidan Shugaban kasar wadda ta samu wakilcin mataimakiyarta ta musamman a kan harkokin mata, Rukayyatu Abdulkareem Gurin, ta kara da cewa, lamarin cinzarafin mata na daya daga cikin abubuwan da aka tattauna a taron kwanaki 16 da aka yi inda waklilai daga kasashen duniya suka samu halarta, musamman ganin mastala ce da ake fama da ita a sassan duniya.

Ta yaba wa matan gwamnonin a kan yadda suka hada kai don ganin an samar da yanayi na kare mata da kananan yara daga cutarwa ta kowacce fuska.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ta ce, “Hanyar samar da daidato da hanyoyin samun aiki ga mata na da matukar muhimmanci, Nijeriya ta yi gaggarumar nasara a wannan fannin, musamman in aka lura da yadda aka zartar da dokar haramta cin zarafin mata ‘ Biolence Against Persons Prohibition (BAPP)’ a wasu jihohi 34 na tarrayar kasar nan.

Ta kuma kara da cewa, kungiyar matan gwamnonin sun kudurin aniyar aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki doin ganin an rage yadda ake cin zarafin mata da kananan yara a kasar nan.

“Yakamata mu kuduri aniyar tabbatar da ganin kowacce mace ko yarinya ta samu ‘yancin rayuwa tare da cikakken kariya daga dukkan abin da zai iya cutar da ita,” in ji ta.
Ana shi jawabin, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Nijeriya, kuma Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal, ya tabbatar wa da mata cewa, gwamnoni za su cigaba da bayar da gudummawar da ta kamata don ganin an kawo karshen cin zarafin mata a Nijeriya.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, saura jihohi 2 da basu sanya hannu a kan dokar kariya ga mata ba za su sa hannu nan ba da dadewa ba, ya kuma yaba wa matan gwamnonin a kan wannan kokarin, da yaba masu a kan yadda suka samar da yanayin shirin zai cigaba koda a bayansu ne.

Tunda farko, shugabar kungiyar na matan gwamnonin Nijeriya kuma uwargidan Gwamnan Jihar Sakkwato, Hajiya Mariya Aminu Tambuwal, ta ce, cikin makasudin kafa kungiyar sun hada da tattara masu ruwa da tsaki don ganin an fuskanci matsalar cin zarafin mata a Nijeriya.

Ita a nata jawabin, Ministar Harkokin Mata, Pauline Tallen, ta yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai a kan dokoki masu tsauri ga masu cin zarafin mata a jihar, a dokar wanda aka sanya wa hannu a watan Satumba 2021, an tanadi yin dandake ga wadanda aka samu da cin zarafin mata.

Dokar da aka yi wa kwaskwarima ta tanadi duk wani magidanci da aka kama ya yi wa yarinya ko yaro da shekarunsa suke kasa da 14 fyade a yi masa dandaka yayin da macen da aka kama ta yi wa ‘yan yara fyade ita ma za a cire mata mahaifa.

Aisha Buhari
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

Ana Sa Ran Cop15 Zai Kai Ga Wani Sabon Matsayi Bayan Yarjejeniyar Paris

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.