ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Sa Ran Tattalin Arzikin Kasar Sin Zai Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya A Shekarar 2023 

by Sulaiman
3 years ago
Arzikin kasar Sin

Baya ga sassauta matakan yaki da annobar COVID-19, tare da la’akari da tsayin daka da karfin tattalin arzikinta, manazarta sun yi imanin cewa, tattalin arzikin kasar Sin, zai farfado a shekarar 2023, kuma zai ci gaba da zama abin dogaro kana muhimmin karfin tattalin arzikin duniya a shekarar 2023. 

Lawrence Loh, darektan cibiyar tafiyar da harkokin mulki da ci gaba mai dorewa a kwalejin koyar da harkokin kasuwanci na jami’ar kasar Singapore, ya shaidawa babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG cewa, duk da yanayin tattalin arzikin duniya da illolin annobar, tattalin arzikin kasar Sin abin a yaba ne matuka a shekarar 2022.

  • Sin: Matakin Amurka Da Daukar Matsayar Kashin Kai Da Kariyar Cinikayya Na Yin Illa Ga Hada hadar Samar Da Hajoji

A ranar Juma’a ne aka kammala babban taron shekara-shekara kan aikin raya tattalin arzikin kasar Sin a birnin Beijing, inda aka tsara ka’idojin raya tattalin arzikin kasar na shekara mai zuwa, da tsara muhimman batutuwan da suka shafi harkokin tattalin arziki na shekara mai zuwa, gami da fadada bukatun cikin gida, da hanzarta gina tsarin masana’antu na zamani, da karfafa hukumomin jin dadin jama’a da kamfanoni masu zaman kansu, da jawo karin jarin waje, da kuma hana aukuwar manyan hadurra na tattalin arziki da kudi.

ADVERTISEMENT

A kwanakin baya, rahotanni daga bankuna da dama na duniya sun yi hasashen cewa, tattalin arzikin kasar Sin, zai samu kyakkyawan sakamako a shekarar 2023, inda Morgan Stanley da Societe Generale, manyan kamfanonin ayyukan hada-hadar kudi na kasa da kasa guda biyu, sun yi hasashen karuwar kashi biyar cikin dari a shekarar 2023.

A halin da ake ciki yanzu, kamfanonin kasashen duniya da dama, suna fadada ayyukansu da zuba jari a kasar Sin. Alkaluman hukuma sun nuna cewa, a cikin watanni 10 na farkon bana, jarin kai tsaye daga kasashen waje da aka zuba a babban yankin kasar Sin, ya karu da kashi 17.4 bisa dari bisa makamancin lokaci na bara, zuwa dalar Amurka biliyan 168.34.(Ibrahim)

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da “Bikin Nuna Al’adun Larabawa”

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da “Bikin Nuna Al’adun Larabawa”

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.