• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Sa Ran Tattalin Arzikin Kasar Sin Zai Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya A Shekarar 2023 

by Sulaiman
3 years ago
Arzikin kasar Sin

Baya ga sassauta matakan yaki da annobar COVID-19, tare da la’akari da tsayin daka da karfin tattalin arzikinta, manazarta sun yi imanin cewa, tattalin arzikin kasar Sin, zai farfado a shekarar 2023, kuma zai ci gaba da zama abin dogaro kana muhimmin karfin tattalin arzikin duniya a shekarar 2023. 

Lawrence Loh, darektan cibiyar tafiyar da harkokin mulki da ci gaba mai dorewa a kwalejin koyar da harkokin kasuwanci na jami’ar kasar Singapore, ya shaidawa babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG cewa, duk da yanayin tattalin arzikin duniya da illolin annobar, tattalin arzikin kasar Sin abin a yaba ne matuka a shekarar 2022.

  • Sin: Matakin Amurka Da Daukar Matsayar Kashin Kai Da Kariyar Cinikayya Na Yin Illa Ga Hada hadar Samar Da Hajoji

A ranar Juma’a ne aka kammala babban taron shekara-shekara kan aikin raya tattalin arzikin kasar Sin a birnin Beijing, inda aka tsara ka’idojin raya tattalin arzikin kasar na shekara mai zuwa, da tsara muhimman batutuwan da suka shafi harkokin tattalin arziki na shekara mai zuwa, gami da fadada bukatun cikin gida, da hanzarta gina tsarin masana’antu na zamani, da karfafa hukumomin jin dadin jama’a da kamfanoni masu zaman kansu, da jawo karin jarin waje, da kuma hana aukuwar manyan hadurra na tattalin arziki da kudi.

A kwanakin baya, rahotanni daga bankuna da dama na duniya sun yi hasashen cewa, tattalin arzikin kasar Sin, zai samu kyakkyawan sakamako a shekarar 2023, inda Morgan Stanley da Societe Generale, manyan kamfanonin ayyukan hada-hadar kudi na kasa da kasa guda biyu, sun yi hasashen karuwar kashi biyar cikin dari a shekarar 2023.

A halin da ake ciki yanzu, kamfanonin kasashen duniya da dama, suna fadada ayyukansu da zuba jari a kasar Sin. Alkaluman hukuma sun nuna cewa, a cikin watanni 10 na farkon bana, jarin kai tsaye daga kasashen waje da aka zuba a babban yankin kasar Sin, ya karu da kashi 17.4 bisa dari bisa makamancin lokaci na bara, zuwa dalar Amurka biliyan 168.34.(Ibrahim)

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
Daga Birnin Sin

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da “Bikin Nuna Al’adun Larabawa”

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da “Bikin Nuna Al’adun Larabawa”

LABARAI MASU NASABA

Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

October 24, 2025
Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

October 24, 2025

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025
An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

October 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025
Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.