ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

by Leadership Hausa
11 months ago
Sule

Ya dawo gida daga Amurka ba, amma ba a matsayin wanda ya yi ritaya ba, illa kawai don sake fasalin jihar baki-ɗaya, musamman ta fuskar inganta masana’antu.

Daga Gudi Zuwa Ɗaukaka

A ƙauyen Gudi, inda suke da al’adu daban-daban tare da zaman lafiya, a nan Abdullahi Sule ya fara koyon horon aiki.

ADVERTISEMENT

An haife shi a ranar 26 ga Disambar 1959, barin garinsu da ke Nasarawa zuwa yunƙurin kawo sauyi a jihar, na da alaƙa da kyakkyawar manufa da kuma hangen nesa.

  • Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa
  • ‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Sai ga shi yau, yaron da fito daga Gudi ya kasance a matsayin mai tsara yadda za a inganta masana’antu a Jihar Nasarawa, kuma shugaba gogagge, wanda ya zagaya duniya tare da sanin matsalolin gida, wannan ne yasa labarinsa ya yi fice a Arewacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Injiniya Mai Matuƙar Hangen Nesa

Tun kafin ya shiga siyasa, Sule ya kasance mutum mai gaskiya da aiki tuƙuru. Bayan kammala karatun digirinsa na farko da na biyu a Amurka, duk a fannin Injiniyarin da Fasahar Masana’antu, B.Sc da M.Sc daga Jami’ar Jihar Indiana, ya kuma haɓaka ƙwarewarsa a manyan kamfanonin injiniya na Amurka, daga Dril-Ƙuip zuwa Kamfanin Osyka, inda ya zama daraktan ci gaban kasuwanci na Afirka da Gabas ta Tsakiya.

Lokacin da ya dawo Nijeriya, a shekara ta 2000, ba kawai da takaddun shaida ya dawo ba, ya dawo ne da cikakkiyar ƙwarewa. Shi ne ya kafa kamfanin mai na Sadiƙ Petroleum, ya jagoranci tafiyar da kamfanin na ‘African Petroleum Plc’, sannan ya zama Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin Siga na Dangote, inda ya yi ƙaurin suna wajen inganci da ƙirƙire-ƙirƙire.

Waɗannan abubuwa, sun ne suka zama ginshiƙan manufar siyasarsa, wajen tafiyar da Jihar Nasarawa; musamman ta fuskar kasuwanci.

Hange Da Dabarunsa Na Aiki

Lokacin da ya kama aiki a matsayin gwamna, Gwamna Sule ya zo da wani shiri, mai suna ‘Nassarawa Economic Deɓelopment Strategy (NEDS)’.

Wannan ita ce cikakkiyar taswirar ci gaban jihar ta farko, wadda aka gina ta a kan masana’antu da samar da ababen more rayuwa, ci gaban kasuwancin al’umma da kuma shugabanci na gari.

NEDS, ta sake fasalin yanayin tattalin arziƙin Jihar Nasarawa, daga yankin noma zuwa wani yanki na saka hannun jari.

A ƙarƙashin jagorancinsa, jihar ta jawo hankalin masu zuba jari na gida da waje a masana’antu, ma’adanai, wutar lantarki da noma, inda ya mayar da Jihar Nasarawa matsayin cibiyar masana’antu ta Nijeriya.

Hasashensa na tattalin arziƙi, na da inganci kamar yadda yake da buri: mayar da fa’idar da jihar ke da ita cikin ma’adanai masu ƙarfi, kusanci da Abuja da yawan sanya matasa yin gasa a tsakaninsu.

Masana’antu A Matsayin Ginshiƙin Ci Gaba

Tsarin mulki na Gwamna Sule, yana ɗaukar masana’antu a matsayin abubuwan more rayuwa. Tun daga fafutukar ci gaban birane da gwamnatinsa ta yi na gina manyan titunan birane zuwa wuraren shaƙatawa na masana’antu a ƙauyen Nasarawa, zuwa ayyukan makamashin da za a sabunta, jihar na ci gaba da zama babbar wata hanya ta zuba jari.

Ta hanyar haɗin gwiwa da gangan, Jihar Nasarawa ta jawo hankalin kamfanoni, domin samar da siminti, ma’adanan lithium, sarrafa ethanol, samar da ayyukan yi, kuɗaɗen shiga da sauransu.

Haɗin gwiwar da jihar ke yi da Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), kan amfani da iskar gas da kafa aikin haƙo mai da iskar Gas na Nasarawa, ya nuna ƙwaƙƙwaran matakai na samun wadatar makamashi da matuƙar ƙima.

Ayyukan Ababen More Rayuwa Da Sha’anin Mulkin

Yunƙurin sabunta ababen more rayuwa na Gwamna Sule, abu ne da ya samo asali. Hanyoyi, Makarantu da asibitoci, sun bazu a ko’ina cikin ƙananan hukumomi, don tabbatar da ganin cewa; ba a bar al’umma a baya ba.

Bayan ayyuka na zahiri, ana ayyana mulkinsa ta hanyar bayyana gaskiya, haɗin gwiwar jama’a da sake fasalin hukumomi.

Gwamnatinsa ta ɓullo da tsarin gudanar da filaye a zamanance, gyare-gyaren haraji wanda ya dace da zuba jari da tsarin PPP, wanda ke taimakawa wajen sauƙaƙa kasuwanci da samun bunƙasarsa.

Yana kuma faɗaɗa bayar da damar ilimi da sana’o’i, domin gina tushen jarin Ɗan’adam, wanda zai ci gaba da ingiza ci gaban masana’antun jihar.

Masanin Makamar Aiki A Mulki

Waɗanda suka san shi, sun bayyana Injiniya Sule ba a matsayin ɗan siyasa ba, illa a matsayin masanin makamar aiki, gogagge, mai kuma tarin ƙwarewa. Ya kawo wa gwamnatin tasa sahihancin injiniya da kuma hazaƙar da ya samu a matsayin manaja.

Tarihinsa- daga Kamfanin ‘Jos Steel Rolling Company’ zuwa na ‘African Petroleum’, sun ba shi ƙwarewar jagoranci da kuma tawali’u, musamman wajen saurarar mutane dangane matsalolinsu.

Sule
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan'uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.