ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
11 months ago
Idanu

Wani matashi mai suna Auwalu Muhammad ya kwaƙule idanuwan ƙannuwarsa ‘yar shekara bakwai a duniya, Rukayya Muhammad, domin yin tsafin neman kuɗi a yunƙurinsa na zama hamshaƙin mai kuɗi. 

Wannan dai na zuwa ne bayan da Boka mai bayar da sa’ar yin kuɗi da ke sanya jama’a ciro sassan jikin mutane kamar idanu da azzakari ya nemi Auwalu da ya ciro idanun yarinyar domin a masa tsafi ya zama mai kuɗi dare guda. 

  • Don Nuna Wa Duniya Kyawawan Al’adunmu Na Kirkiri Manhajar ‘Unlock Arewa’ – Bappi
  • Don Nuna Wa Duniya Kyawawan Al’adunmu Na Kirkiri Manhajar ‘Unlock Arewa’ – Bappi

A halin yanzu likita ya tabbatar da cewar Rukayya ba za ta sake gani ba domin idanuwanta sun lalace gaba ɗaya. 

ADVERTISEMENT

Wannan abun takaici ya faru ne a yankin Wailo da ke ƙaramar hukumar Ganjuwa a jihar Bauchi.

A lokacin da ake zantawa da mahaifin yarinyar ya bayyana cewar wanda ake zargin (Auwalu) ya yaudari ‘yar uwar tasa, wacce suke da iyaye guda tare, zuwa daji tare da kwaƙule mata idanu da ƙarfin tsiya. 

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Mahaifin Rukayya, Muhammad Adamu mazaunin ƙauyen Bayan Dutse da ke Wailo, a gundumar Kubi cikin ƙaramar hukumar Ganjuwa a ranar 17 ga watan Oktoba ya kai rahoton caji ofis ɗin Soro ya ke shaida cewar wani matashi mai suna Auwal Dahiru mai shekara 17, ya kai farmaƙi wa yarsa da ƙoƙarin kasheta da kwaƙule mata idanuwanta. 

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil a ranar Litinin, ya ce, lokacin da ‘yansanda suka samu rahoton faruwar lamarin cikin gaggawa a ƙarƙashin Baturen ɗansanda da ke kula da caji ofis ɗin Soro, CSP Aliyu Mohammad Goni, sun kai agaji inda lamarin ya faru.

A lokacin da aka ɗauki Rukayya zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), Bauchi, domin mata jinya, kwararren likitan Ido a asibitin ya tabbatar da cewar yarinyar ba za ta sake gani da idanuwanta ba har ƙarshen rayuwarta. 

Kan haka ne rundunar ‘yansandan ta ce zuwa yanzu ta cafke mutane shida da ake zargi da hannu kan wannan aika-aikar waɗanda suka haɗa da Auwal Dahiru, mai shekara 17 da ke Bayan Dutse, Wailo, Kubi, Ganjuwa, Mohammed Rabiu (mai shekaru 19), Saleh Ibrahim (20), Nasiru Muhammad mazaunin cikin garin Soro a Ganjuwa, Hassan Garba mazaunin Soro da kuma Garba Dahiru mai shekara 43 a duniya kuma mazaunin Soro.

“Lokacin da ake bincike, waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu,” Wakil ya tabbatar.

Jami’in watsa labaran ‘yansandan ya kuma sanar da cewa yanzu haka bincike na ci gaba da gudana domin zaƙulo dukkanin masu hannu a wannan aikin domin su fuskanci Shari’a. 

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi,  State Command, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci a gaggauta maida binciken kes ɗin zuwa sashin binciken manyan laifukan (SCID), Bauchi domin faɗaɗa bincike da gano wasu abubuwan da suke akwai kan lamarin. 

Ya bayar da tabbacin wanzar da gaskiya da adalci kan lamarin da yin aiki bisa kwarewa.

Idanu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.